Bola Tinubu
Matasan Ijaw sun bukaci shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya yi murabus daga mukamin ministan man fetur. Sun bukaci a ba wanda zai iya aikin yadda ya dace.
Atiku Abubakar, Abdullahi Ganduje da wasu jiga-jigan jam'iyyar APC mai mulki sun halarci jana'izar surukar Nuhu Ribadu, mai ba shugaban kasa shawara kan tsaro.
Babban hafsan sojin Najeriya, Manjo Janar Taoreed Lagbaja ya ce ba za su saurari masu son juyin mulki ba kamar yadda wasu ke ta kiraye-kirayen a yi.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu zai ziyarci kasar China. Shugaba Tinubu zai kai ziyara kasar ne domin tattauna hanyoyin ragewa talakan Najeriya radadi.
Masu fama da ciwon sukari a Najeriya sun koka kan yadda magunguna da kayan abinci ke gagararsu sakamakon tsadar da suka yi. Sun nemi taimakon Shugaba Bola Tinubu.
Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa za ta samar da ayyukan yi ga matasan kasar nan fiye da miliyan 2 a ɓangaren nishaɗi da fasaha ta ma'aikatar fasaha da al'adu.
Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta juyo kan mata inda ta sake ware wani tallafi a jihohin Najeriya 36 da birnin Tarayya Abuja domin taimaka musu a sana'o'insu.
Gwamnatin tarayya ta yi martani ga tsohon shugaban APC, Salihu Lukman kan magana da ya yi a kan hadarin zaben APC da Bola Tinubu a zaben 2027 mai zuwa.
A yayin da hukumar NIMET ta fitar da rahoto kan barnar da ambaliyar ruwa ta yiwa manoma, ministan noma, Abubakar Kyari ya yi magana kan matakin da aka dauka.
Bola Tinubu
Samu kari