Yan ta'adda
Hon. Ahmed Jaha ya ce Boko Haram na amfani da jiragen sama masu sarrafa kansu a Borno. Ya ce sun fi sojoji kayan yaki na zamani. Gagdi ya ce an ƙwace tankoki 40.
Karamin ministan tsaro, Bello Matawalle, ya bayyana cewa an samu nasarar hallaka 'yan ta'adda masu dumbin yawa a karkashin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.
'Wasu 'yan bindiga sun kai sabon hari jihar Filato tsakar dare a lokacin da mutane ke barci. Sun kashe mutane 6 a karamar hukumar Barikin Ladi, sun jikkata da dama.
Yayin da kashe-kashe ya yi yawa a Benue, Majalisar Wakilai ta zargi Gwamna Alia da watsi da dokar hana kiwo a fili, wanda ke haddasa rashin tsaro a jihar.
Boko Haram sun kai hari sansanin sojoji a Buni Yadi, jihar Yobe, inda suka kashe sojoji hudu, suka lalata makamai, motocin yaki da bindigogin rundunar.
Mafarauta da dama sun fada tarkon 'yan ta’addan Lakurawa a dajin Tangaza, inda ake fargabar 13 sun mutu. Sojoji sun dakile wani harin, amma an lalata turken MTN.
Sababbin hare-haren mabiya Bello Turji sun tilasta wa mazauna kauyuka 20 a Sakkwato yin hijira, yayin da matsalar tsaro ke ƙara ta'azzara a yankin.
Yayin da sojoji ke ci gaba da kokarin kakkabe ƴan bindiga, an ruwaito cewa wasu jagororin 'yan bindiga sun yi wata muhimmiyar ganawa a dajin Zamfara.
Rahotanni da muke samu sun tabbatar da cewa ƴan bindiga da ake zargin yaran Bello Turji ne sun kai farmaki garuruwa da ke karamar hukumar Isa a Sokoto.
Yan ta'adda
Samu kari