Yan ta'adda
'Yan ta'addan kungiyar Lakurawa sun kai wani harin ta'addanci a jihar Kebbi. 'Yan ta'addan sun hallaka wani jami'in hukumar kwasfam yayin harin da suka kai.
Wata ƙungiya mai suna Concerned Nigerians for Human Security ta rubuta wa Donald Trump wasiƙa, tana neman ya shiga tsakani kan tsananin rashin tsaro a Zamfara.
’Yan bindiga da ake zargin yaran Bello Turji ne sun kashe mutum biyar tare da sace wasu tara a kauyen Bargaja, karamar hukumar Isa, Jihar Sokoto.
Malamin addinin Musulunci Sheikh Ahmad Gumi ya bayyana cewa duk ganawarsa da ‘yan bindiga ta kasance ne tare da jami’an gwamnati da rundunar ‘yan sanda.
Sheikh Ahmad Gumi ya ce ƴan bindiga ba sa kai hari babu dalili, yana mai kiran gwamnati da ta nemi sulhu da su domin samun zaman lafiya a Najeriya.
Majalisar Wakilai ta yi Allah-wadai da harin da ’yan bindiga suka kai wa konboyin dan majalisa Jafaru Mohammed Ali a Neja, inda jami’an tsaro suka mutu.
Dan gwagwarmaya, Kwamred Osita Obi ya ce yawancin laifuffuka a jihar Anambra da yankin Kudu maso Gabas ‘yan gida ne ke aikatawa, ba baki daga waje ba.
A labarin nan, za a ji cewa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya yi martani ga barazanar takwaransa na Amurka, Donald Trump a kan zargin kisan kiristoci.
Kungiyar ISWAP ta mayar da martani ga kalaman Donald Trump, tana kiran shugaban Amurka “makaryaci kuma dan kama-karya” da ke neman ya ta da rikici a Najeriya.
Yan ta'adda
Samu kari