Yan ta'adda
Mutane biyar daga cikin wadanda 'yan bindiga suka sace a kauyen Dan Isa sun kubuta. An yi jana'izar mutum biyar bayan ban sake gano gawar mutum daya a daji.
Rahotannin da muke samu yanzu na nuni da cewa mahaifiyar fitaccen mawakin siyasa, Dauda Kahutu Rarara ta kubuta daga hannun 'yan bindiga bayan sati uku.
Jama'ar karamar hukumar Dawakin Kudu sun shiga tashin hankali bayan an gano gawarwaki guda shida a gidan wani mai sayar da kayan miya, Abdul-Aziz.
Kakakin majalisar wakilai, Abbas Tajudeen ya bayyana cewa matsalar rashin tsaro a Arewacin Najeriya ta samu asali ne saboda ayyukan hako ma'adanai ba busa ka'ida ba.
Rundunar sojin saman Najeriya ta tabbatar da halaka 'yan bindiga a dajikan kananan hukumomin Giwa da Igabi a jihar Kaduna. Hakan ya faru ne cikin makon da ya gabata.
Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya bayyana harin kunar bakin wake da 'yan ta'adda suka kai a jihar a matsayin kokarin yiwa gwamnatinsa zagon kasa.
Dakarun sojojin Najeriya sun samu nasarar kubutar da wasu mutum 57 da 'yan ta'addan Boko Haram suka sace a dajin Sambisa. Sojojin sun kuma hallaka 'yan ta'adda.
Wasu 'yan ta'adda sun balle gidan gyaran hali a kasar Nijar. Hakan yayi sanadin tserewar daruruwan mayakan ta'addancin Boko Haram da masu safarar kwayoyi.
Hedikwatar tsaro ta DHQ a jiya Alhamis ta ce sojoji sun dakile shirin da ‘yan ta’adda ke yi na lalata wasu muhimman kadarorin Najeriya. DHQ ta yi karin haske.
Yan ta'adda
Samu kari