Yan ta'adda
Wasu matasa sun babbaka gawarwakin wasu da ake zargi yan bindiga ne a jihar Kaduna a Arewacin Najeriya. Sojoji sun kai farmaki ne kan yan bindigar ranar Laraba
Fitaccen lauya, Bulama Bukarti ya kaddamar da asusun tallafawa sojojin da suka hallaka Halilu Sabubu domin nunawa sojojin yan Najeriya suna tare da su.
Malamin Musulunci, Sheikh Musa Yusuf Assadus Sunnah ya tura sako ga Bello Turji da sauran yan ta'adda bayan kisan Halilu Sabubu da safiyar ranar Juma'a.
Hafsan tsaron kasar, Janar Christopher Musa ya ba da kyautar kudi ga dakarun sojoji da suka yi nasarar hallaka dan ta'adda, Halilu Sabubu a Zamfara a jiya Juma'a.
Kwanaki uku kafin hallaka rikakken dan ta'adda, Halilu Sabubu, an wallafa faifan bidiyo inda ya ke rokon yan uwansa kan lamarin tsaro ciki har da Bello Turji.
An kama yan daba 3 da suka yi yunkurin kashe dan sanda a Adamawa. Dan sandan ya yi gumurzu da su yayin da suka yi kokarin masa kwace a cikin Keke NAPEP.
Gwamnatin jihar Zamfara ta bayyana cewa akwai makarkashiya a lamarin tsaron jihar kowa ya sani kuma wasu ne manya a sama da ke siyasantar da shi domin bukatunsu.
A rahoton nan, za ku ji rundunar yan sanda a Kaduna ta yi nasarar fatattakar wasu bata-gari da su ka hada da wasu yan bindiga da yan fashi a jihar.
A wannan labarin, al'ummar Sakkwato sun kara fada wa cikin zullumi biyo bayan yadda yan ta'adda daga kasashen ketare ke yin tururuwa zuwa jihar da mulkarsu.
Yan ta'adda
Samu kari