Surukin Gwamnan Katsina ya bar APC, ya fara kira ga mutane su dawo da PDP kan mulki a 2023

Surukin Gwamnan Katsina ya bar APC, ya fara kira ga mutane su dawo da PDP kan mulki a 2023

  • Alhaji Bishir Audi Kofar Bai ya bayyana cewa ya fice daga jam’iyyar APC mai mulki a jihar Katsina
  • ‘Dan siyasar wanda yace shi ‘danuwan matar gwamna ne, ya koma PDP saboda rashin adalcin APC
  • Bishir Audi Kofar Bai shi ne ya jagoranci kungiyar Buhari/Masari Door-To-Door a zaben da ya wuce

Katsina - Alhaji Bishir Audi Kofar Bai ya bada sanarwar sauya-sheka daga jam’iyyar APC mai mulki, inda ya ce ya bi jam’iyyar hamayya ta PDP a Katsina.

Jaridar Katsina Post tace wannan matashi ya na ikirarin cewa shi kanin matar gwamnan Katsina ne.

Bishir Audi Kofar Bai ya sanar da Duniya ya bar APC a gaban daruruwan ‘ya ‘yan jam’iyyar adawa da magoya baya a ranar Asabar, 18 ga watan Disamba, 2021.

Kara karanta wannan

Rubutu a Facebook: Kotu ta bada belin hadimin Goje bayan tsare shi tsawon kwana 20

Rahoton yace hakan ya zo daidai lokacin da PDP ta kaddamar da shirin yi wa ‘ya ‘yanta rajistan zamani a sakatariyarta a karamar hukumar Birnin Katsina.

Audi Kofar Bai : Da mu aka yi wahala a baya

Baya ga zamansa na ‘danuwan matar gwamna, Bishir Audi Kofar Bai yace shi ne shugaban tafiyar nan ta Buhari/Masari Door-To-Door a zaben 2019 da ya wuce.

Gwamnan Katsina
Gwamna Ganduje, Tambuwal da Masari Hoto: abbas.sflani
Asali: Facebook

Da yake bayanin dalilin ficewarsa daga APC da ya yi wa hidima a baya, Alhaji Bishir Audi Kofar Bai yace jam’iyyar ba ta da adalci, yace gumin da suka yi duk a banza.

Wannan ‘dan siyasa yace ba ayi la’akari da kokarin da suka yi wajen kafa APC a jihar Katsina da ma kasa baki daya ba, yace gwamnati ba ta taimake shi da komai ba.

Kara karanta wannan

Wata sabuwa: Kotu ta soke kasancewar dan takarar APC a zaben gwamnan Anambra

A jawabinsa na farko ga jama’a a matsayin ‘dan PDP, Audi Kofar Bai ya yi kira ga jama’a su dage wajen ganin jam’iyyar APC ta sha kashi a babban zabe mai zuwa na 2023.

Audi Kofar Bai ya roki jama’an Katsina su yi kokarin ganin PDP ta dawo kan mulki a jihar. Tun 1999 jam’iyyar PDP ke rike da jihar ta Katsina, sai a 2015 lamarin ya canza.

An yi wa Alhaji Bishir Audi rajista, kuma ya nunawa Duniya katinsa na zama cikakken ‘dan PDP.

An ci amanar Tinubu a APC?

Kwanan nan aka ji cewa daya daga cikinmanyan ‘Yan Buhariyya a kudancin Najeriya, Osita Okechukwu, ya karyata littafin Bisi Akande da aka kaddamar a Legas.

A cewar Okechukwu, Bola Tinubu ya taimaka wajen ba Muhammau Buhari nasara, amma babu wata yarjejeniya da aka yi na za a ba shi mataimakin shugaban kasa.

Asali: Legit.ng

Online view pixel