Yayin da Ake Jiran Bayani, Sanatoci Sun Yi Shiru Kan Batun Tsige Shugaba Buhari
- Majalisar dattawa ta yi tsit game da batun tsige Buhari, duk da a baya wasu sanatoci sun ba shugaban wa'adin kawo karshen matsalar tsaro
- Majalisar dattawa ta yi hutun wani dan lokaci, inda ta dawo ci gaba da zaman majalisa a cikin makon nan
- 'Yan Najeriya na ci gaba da shiga damuwa kasancewar yadda batun tsaro ke kara zama mummuna a kwanakin nan
FCT, Abuja - Sanatoci a Najeriya sun ci gaba da zaman majalisa a ranar Talata 20 ga watan Satumba, amma sun yi shuru game da batun kawo karshen zaman Shugaba Muhammadu Buhari a kujerar mulkin Najeriya.
Idan baku manta ba, sanatoci daga jam'iyyun adawa daban-daban sun tada batun ko dai Buhari ya gyara lamarin tsaron Najeriya ko kuma su tsge shi, Punch ta ruwaito.

Kara karanta wannan
Yajin aiki: An cimma matsaya tsakanin ASUU da majalisa, za a kai batu gaban Buhari kafin a koma makaranta
Majalisar ta ba Buhari wa'adin makwanni shida ya tabbatar ya kawo karshen matsalar rashin tsaro, kana kasa ta zauna lafiya.

Asali: UGC
Bayan an dawo zaman majalisa, babu sanatan da ya kawo batun a zauren majalisa, kuma babu wanda ya yi magana da manema labarai kan batun.
Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!
Madadin magana game da tsige Buhari, Ahmad Lawan ya dago batun tsaro inda yace:
"'Yan uwa abokan aiki, kafin mu tafi hutu, majalisar sanatoci ta nuna matukar damuwa game da lamarin tsaron kasar nan. We yi tattaunawa game da kalubalancin tsaro a kasar nan."
Hakazalika, ya bayyana cewa, majalisar ta zauna da masu ruwa da tsaki a fannin tsaron Najeriya, kuma an tattauna don nemo mafita mai daurewa ga matsalolin tsaro.
Ana samun nasara a fannin tsaro
Da yake karin haske, ya ce hukumomin tsaro suna samun nasarar shawo kan matsalar tsaro, inda ya ba da tabbacin cewa za a samu ci gaba mai daurewa, rahoton kafar labarai ta ReubenAbati.

Kara karanta wannan
Cefanar da NNPCL: 'Yan Najeriya ba Zasu Fuskanci Wuyar Man Fetur ba a Watan Disamba
"Daga bayanan da suka tabbata, hukumomin tsaronmu na samun nasara sosai kuma lamarin na samun sauki."
A bangare guda, ya ce majalisar dattawa za ta ci gaba da kai komo da tattaunawa da hukumomin tsaro domin sanin halin da ake ciki.
A wani labarin, wa'adin makwanni shida da aka dibarwa shugaban kasa Muhammadu Buhari ya warware matsalolin tsaron Najeriya sun shude, har yanzu abubuwa basu kankama ba.
A cewar rahoton jaridar The Guardian, majalisar dokokin Najeriya za ta sake zama a ranar Talata mai zuwa, 20 ga watan Satumba don sake duba batun tsige shugaban.
Idan baku manta ba, rahotanni sun karade Najeriya a ranar 27 ga watan Yuli cewa, majalisar dattawa ta dago batun tsige Buhari saboda ta'azzarar lamurran tsaro.
Asali: Legit.ng