Wata mata a Nasarawa: Dalilin da yasa na amince 'dan da na haifa ya dirka min ciki

Wata mata a Nasarawa: Dalilin da yasa na amince 'dan da na haifa ya dirka min ciki

  • Wata mata mai suna Matina Agawua ta ce ta nemi dan cikinta domin tabbatar da ko tana haihuwa
  • Matina ta ce bayan mutuwar mijinta na farko ta shafe tsawon shekaru 15 kafin ta sake aure, kuma da ta yi sun shafe shekaru 6 ba tare da haihuwa ba
  • Ta ce sai ana ta ganin kamar daga wajen ta ne matsalar yake ita kuma tana son mijinta, wannan ne ya sa ta tara da danta da ta samu a auren farko har ta kai ga samun ciki

Nasarawa - Wata mutuniyar Yelwata da ke jihar Nasarawa, Matina Agawua, ta magantu kan dalilin da yasa ta aikata abun Allah-wadai.

A wata hira da jaridar The Nation, Agawua ta ce a lokacin da ta rasa mijinta na farko, sai ta yanke shawarar ci gaba da zama babu aure har tsawon shekaru 13.

Kara karanta wannan

Budurwa ta bi Saurayi a Wurin Biki ta Tashe shi, Zai Aureta Bayan Shekaru Uku a Bidiyo

Wata mata a Nasarawa: Dalilin da yasa na amince da na ya dirka min ciki
Wata mata a Nasarawa: Dalilin da yasa na amince da na ya dirka min ciki Hoto: punchng.com
Asali: UGC

Ta ce bata samu ciki ba a auren wanda ya dauki tsawon fiye da shekaru shida.

Matar ta ce surukanta sun yi barazanar korata waje kan hujjar cewa bata haihu da dansu ba.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Matina ta ce:

“Mun yi aure sama da shekaru shida amma har yanzu bamu samu haihuwa ba saboda matsalar mijina, kamar yadda rahoton likita ya nuna, sannan kuma ina ta jin wai-wai yana shirin kara mata ta biyu saboda na kasa haifar mai da.”

Ta ce a yayin da ta yi gwajin haihuwa, mijinta bai damu da ya je ganin likita don sanin daga ina matsalar take ba.

Daily Trust ta rahoto cewa matar ta ce tana zargin mijin na fama da matsalar karancin maniyi ne wanda yasa ya gaza zama uba domin dai gwaji ya nuna babu abun da ya same ta.

Kara karanta wannan

Abin kunya: Mata ta kama mijinta dumu-dumu yana lalata da kanwarta da saura wata 3 aurenta

Matar ta ce a tsaka da wannan rikicin ne ta kwanta da da daya tilo da ta samu daga aurenta na farko.

Ta kara da cewar domin tabbatar da cewar tana haihuwa, sai ta yanke shawarar amfani da danta, dalini a Akwanga cikin sirri.

Ta ce:

“Hankalinsa bai kwanta mu je gwajin lafiya ba kan hasashen cewa babu abun da ke damunsa, sai na yanke shawarar lallaba dana, wanda ke da shekaru 16 kuma yake makaranta a Akwanga.
“Ina yawan kai masa ziyara. Yana zama a wani gida tare da yan uwana, don haka ina zuwa na dan zauna da su na dan lokaci, musamman a karshen mako idan bana da zuwa kasuwa.
“Abune mai matukar wahala Tarawa da dan cikina, amma yanayi ya tursasa ni shiga ciki. Ina bukatar tabbatar da ko zan iya haihuwa.
“Na san mijina sosai. Idan ya gano ina alaka da wani namiji a waje, zai kashe ni.

Kara karanta wannan

Duk da Mahaifinta Yace Mummuna ce, Zata Aura Hamshakin Mai Arziki Bayan Aurenta 2 da Yara 7

“Ina kaunarsa sosai kuma ina tsoronsa, don haka mugun nufin yay i ta yawo a zuciyana don sanin ko ina haihuwa. Na yi kokarin ziyartan dana a Akwanga musamman idan n agama al’ada. Na yanke shawarar jan shi a jiki. Muka shaku sannan muka tara.
“Wata rana bayan na gama al’ada, sai na ziyarce shi. Da misalin karfe 11 na dare. Na rike hannunsa sannan na sa ya zauna kusa da ni.
“Na tambaye shi ko ya taba sanin ya mace sai yace dani a’a. na rungume shi. A wannan karon, na ji dumi kuma ina tunanin shima ya ji hakan. Bayan wannan dare, sai kunya ya kamani, na kuma dunga jin cewa na aikata sabo da dana.
“Haramun ne, amma na gargade shi a kan ya boye shi ya zama sirri.”

Mutane su gama aibatani a zo ranar lahira su ga na shige Aljanna na barsu - Umma Shehu

Kara karanta wannan

Budurwa ta Kwace Motar da ba Saurayinta bayan Shekatu 2 da Suka Rabu, Kazantar da ta Gani Ciki ta Tada Hankali

A wani labari na daban, shahararriyar jarumar masana’antar shirya fina-finan hausa ta Kannywood ta yi tsokaci a kan aibata ta da wasu mutane ke yi, sakamakon kallo da suke yi mata a matsayin mai aikata sabon Ubangiji.

A wani bidiyo da sashin Hausa na BBC ya fitar, an jiyo jarumar tana fadin cewa ita da zunubinta ta damu ba da na wani ba sannan kuma cewa duk a laifukan da take aikatawa bata hada Allah da wani.

Asali: Legit.ng

Online view pixel