An rasa rayuka, an sace wasu yayin da ‘Yan bindiga suka yi ta’adi a titin Zaria zuwa Kaduna

An rasa rayuka, an sace wasu yayin da ‘Yan bindiga suka yi ta’adi a titin Zaria zuwa Kaduna

  • Miyagun ‘Yan bindiga sun yi barna a titin Kaduna zuwa garin Zaria a yammacin ranar Litinin dinnan
  • Ana zargin mutane da-dama sun mutu a wannan hari da aka kai, sannan an yi garkuwa da Bayin Allah
  • Wata majiya tace sojoji sun yi kokari wajen kubuto wasu daga cikin wadanda aka nemi ayi gaba da su

Kaduna - Matafiya da-dama sun gamu da tashin hankali a sa’ilin da ‘yan bindiga su ka tare titin Kaduna-Zaria a cikin daren ranar Litinin, 13 ga watan Disamba.

Legit.ng Hausa ta samu labari an kashe mutane, sannan kuma an yi garkuwa da wasu a sakamakon mummunan harin da ‘yan bindiga suka kai a jiya.

Kamar yadda jaridar Daily Nigerian ta tabbatar da rahoton dazu da safe, ‘yan bindigan sun yi ta’adi a daidai unguwar Kofar Gayan da ke bakin shigowa garin Zaria.

Kara karanta wannan

Jami'an tsaro sun kai farmaki sun kamo 'yan bindiga 30, sun ceto wani sarki da aka sace

Miyagun ‘yan bindigan sun tare masu bin hanyar na Kaduna zuwa Zaria ne da kimanin karfe 8:00 na dare, da nufin su yi garkuwa da Bayin Allah, su karbi fansa.

Sojoji sun ceto wasu matafiyan

Wasu wadanda abin ya faru a gaban idanunsu, sun ce miyagun sun kama fasinjoji da dama, suka shiga cikin jeji da su, kafin zuwan jami’an sojoji da suka ceto wasu.

Titin Zaria-Kaduna
Hanyar Kaduna-Zaria Hoto: premiumtimesng.com
Asali: UGC

Wani daga cikin fasinjoji ya shaidawa Daily Nigerian cewa an dauki mutane, kuma an harbe wasu. Sojoji sun ceto wasu daga cikin wadanda aka dauke.

A halin yanzu ana fama da matsalar rashin tsaro tsakanin wannan yanki har zuwa garin Jaji a jihar Kaduna, inda ake da dakarun sojojin kasa rututu a jibge.

Mutum daya ya mutu a harin

Kara karanta wannan

'Yan bindiga daga Zamfara sun kutsa Filato, sun kai farmaki, sun hallaka mutane 10

Wata majiya tace mutanen da aka dauke a hanyar za su haura 30, ta kuma ce an hallaka mutum daya.

Da yake bayani a Facebook, wani Bawan Allah mai suna Nura Lawal Abubakar, ya tabbatar da mutuwar Alhaji Sani Dogara a wannan hari da aka kai a jiya.

Heenatuh Bint Rasheed tace ta na cikin wadanda suka sha da kyar daga hannun ‘yan bindigan.

“Kaduna - Zaria high way mun Sha.... Inna lillahi wa Inna ilaihi rajiun.... Allah ka kubutar da Wanda aka kwashe....”
“ArewaIsBleeding, #MyArewa, #SecureNorth.”

- Heenatuh Bint Rasheed

Zuwa yanzu babu labarin adadin wadanda aka sace, hallaka ko aka ji wa rauni a harin. Jami’an ‘yan sanda na reshen jihar Kaduna ba su yi magana ba tukuna.

Asali: Legit.ng

Online view pixel