An rasa rayuka, an sace wasu yayin da ‘Yan bindiga suka yi ta’adi a titin Zaria zuwa Kaduna

An rasa rayuka, an sace wasu yayin da ‘Yan bindiga suka yi ta’adi a titin Zaria zuwa Kaduna

  • Miyagun ‘Yan bindiga sun yi barna a titin Kaduna zuwa garin Zaria a yammacin ranar Litinin dinnan
  • Ana zargin mutane da-dama sun mutu a wannan hari da aka kai, sannan an yi garkuwa da Bayin Allah
  • Wata majiya tace sojoji sun yi kokari wajen kubuto wasu daga cikin wadanda aka nemi ayi gaba da su

Kaduna - Matafiya da-dama sun gamu da tashin hankali a sa’ilin da ‘yan bindiga su ka tare titin Kaduna-Zaria a cikin daren ranar Litinin, 13 ga watan Disamba.

Legit.ng Hausa ta samu labari an kashe mutane, sannan kuma an yi garkuwa da wasu a sakamakon mummunan harin da ‘yan bindiga suka kai a jiya.

Kamar yadda jaridar Daily Nigerian ta tabbatar da rahoton dazu da safe, ‘yan bindigan sun yi ta’adi a daidai unguwar Kofar Gayan da ke bakin shigowa garin Zaria.

Miyagun ‘yan bindigan sun tare masu bin hanyar na Kaduna zuwa Zaria ne da kimanin karfe 8:00 na dare, da nufin su yi garkuwa da Bayin Allah, su karbi fansa.

Sojoji sun ceto wasu matafiyan

Wasu wadanda abin ya faru a gaban idanunsu, sun ce miyagun sun kama fasinjoji da dama, suka shiga cikin jeji da su, kafin zuwan jami’an sojoji da suka ceto wasu.

Titin Zaria-Kaduna
Hanyar Kaduna-Zaria Hoto: premiumtimesng.com
Asali: UGC

Wani daga cikin fasinjoji ya shaidawa Daily Nigerian cewa an dauki mutane, kuma an harbe wasu. Sojoji sun ceto wasu daga cikin wadanda aka dauke.

A halin yanzu ana fama da matsalar rashin tsaro tsakanin wannan yanki har zuwa garin Jaji a jihar Kaduna, inda ake da dakarun sojojin kasa rututu a jibge.

Mutum daya ya mutu a harin

Wata majiya tace mutanen da aka dauke a hanyar za su haura 30, ta kuma ce an hallaka mutum daya.

Da yake bayani a Facebook, wani Bawan Allah mai suna Nura Lawal Abubakar, ya tabbatar da mutuwar Alhaji Sani Dogara a wannan hari da aka kai a jiya.

Heenatuh Bint Rasheed tace ta na cikin wadanda suka sha da kyar daga hannun ‘yan bindigan.

“Kaduna - Zaria high way mun Sha.... Inna lillahi wa Inna ilaihi rajiun.... Allah ka kubutar da Wanda aka kwashe....”
“ArewaIsBleeding, #MyArewa, #SecureNorth.”

- Heenatuh Bint Rasheed

Zuwa yanzu babu labarin adadin wadanda aka sace, hallaka ko aka ji wa rauni a harin. Jami’an ‘yan sanda na reshen jihar Kaduna ba su yi magana ba tukuna.

Asali: Legit.ng

Online view pixel