Latest
Uwargidan shugaban Amurka, Melania Trump ta fito fili ta musanta duk wata alaka da Jeffrey Epstein, tana cewa zarge-zargen da ake yadawa gaba daya karya ne.
Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya yi magana kan matsalolin da suka addabi Najeriya. Obasanjo ya ba da shawara kan hanyar da za a bi don gyara kasar.
Ofishin jakadancin Amurka a Najeriya ya soki duk wata bukatar biza da yan kasar nan suka nema, ya maida ayyukansa zuwa ofishin Amurka da ke jihar Legas.
Babban Bankin Najeriya (CBN) ya karyata hoton takardar N5,000 mai ɗauke da fuskar Shugaba Bola Tinubu da ke yawo, inda ya ce labarin ƙarya ne babu gaskiya.
Shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawa, Sanata Abba Moro, ya yi magana kan rikicin da ya addabi jam'iyyar PDP wanda ya kawo rarrabuwar kawuna a cikinta.
Tsohuwar jakadiyar Pakistan, Maleeha Lodhi ta yabawa matakin gwamnatin Donald Trump na sanya mataimakin shugaban kasa a tawagar tattaunawa da Iran.
Gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta bayar da kwangilar gina tashar solar ta N3.8bn a Jami'ar Aliko Dangote, da ke Wudil, jihar Kano don magance matsalar wutar lantarki.
Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya umurci fara tattaunawar zaman lafiya da Lebanon cikin gaggawa, ciki har da batun kwance damarar kungiyar Hezbollah.
Rundunar sojojin Najeriya ta tabbatar da cewa jami'anta sun fafata da 'yan ta'adda a jihar Borno. Ta bayyana cewa wasu sojoji sun kwanta dama a harin.
Masu zafi
Samu kari