Tsufa na damun shi: Don ya bayar da dalilai 4 da suka sa IBB ya caccaki Buhari, Atiku da Tinubu

Tsufa na damun shi: Don ya bayar da dalilai 4 da suka sa IBB ya caccaki Buhari, Atiku da Tinubu

  • Ibrahim Babangida ya shiga takaddama lokacin da yayi magana game da zaben shugaban kasa na 2023, yaki da cin hanci da rashawa na Buhari da sauran batutuwa
  • Abubakar Umar Kari, malamin jami’a, ya ce tsohon shugaban kasar na mulkin soja yana da dalilansa na bayyana ra’ayinsa kan batutuwan da ake muhawara a kai
  • Kari ya ce IBB ya kai hari kai tsaye kan yaki da cin hanci da rashawa na Buhari lokacin da ya ce gwamnatinsa tsaftattaciya ce idan aka kwatanta da gwamnati mai ci

Wani farfesa a fannin ilimin halayyar dan adam, Jami’ar Abuja, Dakta Abubakar Umar Kari, ya yi tsokaci kan hirar da tsohon shugaban kasa na mulkin soja, Ibrahim Badamasi Babangida ya yi.

Babangida, wanda aka fi sani da IBB, ya yi magana kan yaki da cin hanci da rashawa da gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari ke jagoranta, kudirin shugabancin Atiku Abubakar da Bola Tinubu, da sauran batutuwa.

Kara karanta wannan

Ta'addanci: IBB ya bayyana manyan kalubale 2 da rundunar sojojin Najeriya ke fuskanta

Tsufa na damun shi: Don ya bayar da dalilai 4 da suka sa IBB ya caccaki Buhari, Atiku da Tinubu
IBB ya yi magana kan yaki da rashawa da kuma zaben 2023 Hoto: GEORGES GOBET/AFP
Asali: Getty Images

A hirar da Daily Trust ta yi da shi, Kari ya ce IBB yana sane da cewa matsayinsa kan dukka batutuwan zai haifar da takaddama.

Ya bayar da dalilansa kan abun da ya sa tsohon shugaban kasar na mulkin soji ya caccaki Buhari, Tinubu da Atiku.

Babangida ya tsufa

A cewar Kari, IBB yana da ikon sukar kowa saboda shekarun sa.

Ya bayyana cewa:

"Amma kuma, IBB na yau ya tsufa, saboda haka zai iya samun damar caccakar kowa."

Tabbatar da ayyukansa ya zama maimaici

Mataimakin farfesa ya yi imanin Babangida yana kokarin ci gaba da kokarinsa na kare wasu ayyukan da ya yi ko ya kasa yi a lokacin gwamnatinsa.

Ya kara da cewa hujjar da IBB ya bayar na soke zaben shugaban kasa na ranar 12 ga Yuni, 1993 ya zama maimaici, kuma abin mamaki, yadda yake maimaitawa, mutane kalilan ne suka yarda da shi.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Buhari ta bayyana dalilin da yasa ba za ta tattauna da 'yan bindiga ba

Domin yakar wadanda ke zargin sa da cin hanci da rashawa

Kari ya lura cewa matsayin tsohon shugaban kasar a kan cin hanci da rashawa ya yi kama da yunƙurin ƙalubalantar waɗanda ke tuhumar sa da laifin cin hanci da rashawa.

Babangida ya yi alfahari da cewa gwamnatinsa ta yi kokari wajen yakar babban makiyi - cin hanci da rashawa.

Ya lura cewa idan aka kwatanta gwamnatinsa da na yanzu, 'yan Najeriya za su gano cewa shi da membobin majalisarsa a lokacin tsarkaka ne.

Da yake martani kan wannan, Kari ya ce:

"Wannan ikirarin ya kasance suka kai tsaye ga yaki da cin hanci da rashawar Shugaba Buhari, wanda ya lalace sosai, musamman a 'yan shekarun nan."

IBB ya inganta ra'ayin “sabon-jini” a lokacin gwamnatinsa

Kari ya lura cewa kalaman Babangida akan Atiku da Tinubu ba bakon abu bane. A cewarsa, tsohon shugaban koyaushe yana haɓkaka ra'ayin "sabon-jini."

Kara karanta wannan

Bakare: Abokin tafiyar Buhari ya ba shi shawarar abin yi, ya daina sukar shugabannin baya

Jami'in ya ce:

"Ya haramta wa wadanda ya kora a matsayin tsoffin 'yan siyasa yin takara don neman mukamai a karkashin jam'iyyu biyu da ya kafa a yayin da yake kan mulki."

Ya kara da cewa IBB yana kuma sane da cewa 'yan Najeriya na fatan samun canji daga tsoffin 'yan siyasa irin su Tinubu da Atiku da ke mulkin kasar.

Tsohon shugaban kasa na mulkin soja IBB ya yi waje da Atiku, Tinubu daga zaben 2023

A baya mun kawo cewa sohon Shugaban kasa a mulkin soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, ya bayyana dalilin da ya sa bai kamata 'yan Najeriya su zabi tsofaffin 'yan siyasa ba a 2023.

Babangida, wanda ake kira IBB, ya fada a ranar Juma'a, 6 ga watan Agusta, cewa kasar na bukatar wani matashi mai kwazo da zai karbi mulki daga hannun Buhari.

Asali: Legit.ng

Online view pixel