Sabbin mutane 126 sun kamu da Korona, yayinda ake gab da isa 60,000
Hukumar hana Yaduwar Cututtuka ta Najeriya wato NCDC ta bayyana cewa annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 126 a fadin Najeriya.
Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da hukumar NCDC ta fitar da misalin karfe 11:na daren ranar Juma'a 2 ga watan Oktoba, shekarar 2020.
A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa an samu karin sabbin mutane 153 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka:
Lagos-62
Rivers-22
Ogun-9
Plateau-7
FCT-7
Osun-5
Kwara-5
Taraba-3
Bayelsa-2
Abia-2
Zamfara-1
Imo-1
Jimillan wadanda suka kamu: 59,127
Jimillan wadanda aka sallama: 50,593
Adadin wadanda suka yi wafati: 1,112
KU KARANTA: Da yiwuwan PPMC ta rage farashin man fetur wannan watan
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng