Zaben Edo: Obaseki ya dauki hanyar nasara yayinda INEC ke shirya sauran sakamakon
- Hukumar INEC ta saki sakamakon zaben kananan hukumomi 13 a jihar Edo
- Gwamna Godwin Obaseki ya lashe kananan hukumomi 11 yayinda Ize-Iyamu ya ci 2 kacal
- Har yanzu ana sauraron sakamakon sauran kananan hukumomin biyar
Sakamakon da hukumar gudanar da zaben kasan watau INEC ya nuna cewa gwamnan jihar Edo mai ci yanzu, Godwin Obaseki, ne kan gaba da tazarar kuri'u kimanin dubu dari tsakaninsa da na biye da shi, Osagie Ize-Iyamu, na jam'iyyar All Progressives Congress (APC).
Legit.ng ta ruwaito muku cewa an gudanar da zaben gwamnan jihar ne ranar Asabar, 19 ga Satumba, kuma hukumar INEC na tattara sakamakon yanzu.
Channels TV ta ruwaito cewa an sanar da sakamakon kananan hukumomi 13 kuma Obaseki ya lashe guda 11 yayinda abokin hamayyarsa ya ci biyu.
Har yanzu ba'a sanar da sakamakon sauran kananan hukumomin ba.
Jihar Edo na da kananan hukumomi 18.
KU KARANTA: Mai gida ya kashe 'yar haya saboda N11,000
Ga jerin wadanda aka sanar:
1. Karamar hukumar Igueben
APC: 5,189
PDP: 7,870
2. Karamar hukumar Esan ta Arewa maso gabas
APC 6559
PDP 13,579
3. karamar hukumar Esan ta tsakiya
PDP: 10,694
APC: 6,719
4. Karamar hukumar Ikpoba Okha
PDP: 41, 030
APC: 18, 218
5. Karamar hukuma Owan ta gabas
APC: 19,295
PDP: 14,7626.
6. Karamar hukumar Estaka West
APC: 26,140
PDP: 17,959
7. karamar hukumar Egor
APC: 10, 202
PDP: 27, 621
8. Karamar hukumar Esan ta yamma
APC - 7,189
PDP - 17,433
9. karamar hukumar Uhunmwonde
PDP: 10,022
APC: 5,972
10. Karamar hukumar Ovia ta Arewa
APC - 9907
PDP - 16, 987
11. Karamar hukumar Esan south East
APC: 9,237
PDP: 10,563
12. Karamar hukumarsa Oredo
APC: 18,365
PDP: 43,498
13. Karamar hukumar Owan West
APC - 11,193
PDP - 11,485
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng