Da dumi-dumi: Yan Najeriya 131 sun kamu da cutar Korona yau
Hukumar hana Yaduwar Cututtuka ta Najeriya wato NCDC ta bayyana cewa annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 131 a fadin Najeriya.
Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da hukumar NCDC ta fitar da misalin karfe 11:na daren ranar Alhamis 17 ga Satumba, shekarar 2020.
A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa an samu karin sabbin mutane 131 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka:
Lagos-45
Kaduna-17
Plateau-17
FCT-16
Delta-6
Niger-6
Kwara-5
Oyo-3
Akwa Ibom-2
Cross River-2
Ekiti-2
Enugu-2
Osun-2
Sokoto-2
Bauchi-1
Ebonyi-1
Katsina-1
Rivers-1
Jimillan wadanda suka kamu: 56,735
Jimillan wadanda aka sallama: 48,092
Adadin wadanda suka yi wafati: 1,093
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng