Yanzu yanzu: Sabbin yan Najeriya 155 sun kamu da cutar Korona
Hukumar Dakile Yaduwar Cututtuka ta Najeriya wato NCDC ta bayyana cewa annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 155 a fadin Najeriya.
Yanzu jihar Plateau ya shiga jerin manyan jihohi biyar masu mafi yawan masu cutar a najeriya
Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da hukumar NCDC ta fitar da misalin karfe 11:na daren ranar Litinin 7 ga Satumba, shekarar 2020.
A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa an samu karin sabbin mutane 125 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka:
Lagos-42
Plateau-25
Rivers-16
Ebonyi-10
Abia-9
Ogun-9
FCT-9
Osun-7
Katsina-6
Kaduna-6
Ekiti-4
Taraba-4
Edo-3
Anambra-2
Akwa Ibom-2
Kano-1
55,160 sun kamu
43,231 aka sallama
1,061 sun mutu
KU KARANTA: Ya zama dole a dakatar da wannan haukan – Sultan ya yi magana kan kashe-kashen kudancin Kaduna
A bangare guda, Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bayyana cewa ta “kashe kudi N30,540,563,571.09, wanda ya yi daidai 84% na naira biliyan 36.3 na kudaden jama’a da gudunmawar da ta karba domin magance lamarin kororna tsakanin 1 ga watan Afrilun 2020 da 31 ga watan Yulin 2020, kudin da ya yi saura a yanzu naira biliyan 5.9 ne.”
Babban ma’ajin gwamnatin tarayya, Agmed Idris, ya bayyana hakan a yayinda yake amsa bukatar da kungiyoyin Socio-Economic Rights and Accountability Project (SERAP) da Connected Development (CODE) suka nema mai kwanan wata 10 ga Agustan 2020.
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng