Da duminsa: Kwana uku jere jihar Flato na zarce Legas yayinda sabbin mutane 296 suka kamu da Korona a Najeriya
Hukumar Dakile Yaduwar Cututtuka ta Najeriya wato NCDC ta bayyana cewa annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 296 a fadin Najeriya.
Kwana uku a jere yanzu jihar Plateau na zarce Legas da Abuja wajen yawan adadin sabbon wadanda suka kamu da cutar.
Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da hukumar NCDC ta fitar da misalin karfe 11:30 na daren ranar Alhamis 27 ga Agustan shekarar 2020.
A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa an samu karin sabbin mutane 296 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka:
Plateau-85
Enugu-46
Oyo-31
Lagos-21
Rivers-20
FCT-15
Kaduna-13
Bauchi-12
Delta-11
Ekiti-11
Akwa Ibom-7
Ebonyi-6
Kwara-5
Ogun-4
Osun-4
Gombe-3
Niger-2
53,317 suka kamu a Najeriiya
40,726 aka sallama
1,011 sun rigamu gidan gaskiya
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng