Da duminsa: Sabbin mutane 252 sun kamu da cutar coronavirus a Najeriya
Hukumar Dakile Yaduwar Cututtuka ta Najeriya wato NCDC ta bayyana cewa annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 252 a fadin Najeriya.
Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da hukumar NCDC ta fitar da misalin karfe 11:30 na daren ranar Talata 24 ga Agustan shekarar 2020.
A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa an samu karin sabbin mutane 252 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka:
Plateau-50
Enugu-35
Rivers-27
Lagos-26
FCT-18
Kaduna-18
Ekiti-10
Kano-10
Taraba-9
Anambra-8
Edo-8
Oyo-8
Delta-7
Ogun-6
Abia-5
Bayelsa-5
Ebonyi-1
Osun-1
Gaba daya:
52,800 jimilan wadanda suka kamu
39,964 aka sallama
1,007 sun mutu
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng