Da duminsa: Sabbin yan Najeriya 373 sun kamu da Coronavirus

Da duminsa: Sabbin yan Najeriya 373 sun kamu da Coronavirus

Hukumar Takaita Yaduwar Cututtuka ta Najeriya wato NCDC ta bayyana cewa annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 373 a fadin Najeriya yau Alhamis.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da hukumar NCDC ta fitar da misalin karfe 11:37 na daren ranar Alhamis 13 ga Agustan shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta a shafinta na Twitter, ta bayyana adadin wadanda suka kamu da cutar a jihohin Najeriya kamar haka:

Da duminsa: Sabbin yan Najeriya 373 sun kamu da Coronavirus
Da duminsa: Sabbin yan Najeriya 373 sun kamu da Coronavirus
Asali: Twitter

Lagos-69

Osun-41

Kaduna-40

Oyo-40

FCT-35

Plateau-22

Rivers-19

Kano-17

DUBA WANNAN: Zulum ya naɗa sabon shugaban ma'aikatan fadarsa

Ondo-17

Ogun-15

Abia-14

Gombe-12

Imo-9

Enugu-7

Kwara-6

Delta-5

Niger-2

Borno-1

Bauchi-1

Nasarawa-1

Alkalluman da hukumar ta dakile cututtukan ta fitar a ranar Alhamis 13 ga Agustan shekarar 2020 ya nuna cewa jimillar wadanda suka kamu da cutar ta korona a Najeriya ya kai 48,116.

An sallami mutum 34,309 bayan an tabbatar da sun warke sarai, a yayin da cutar ta kashe jimillar mutane 966.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164