Karin 'yan Najeriya 290 sun kamu da korona, jimilla 46,867

Karin 'yan Najeriya 290 sun kamu da korona, jimilla 46,867

Hukumar Dakile Yaduwar Cututtuka ta Najeriya wato NCDC ta bayyana cewa annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 290 a fadin Najeriya.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da hukumar NCDC ta fitar da misalin karfe 11:27 na daren ranar Litinin 10 ga Agustan shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa an samu karin sabbin mutane 290 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka:

Karin 'yan Najeriya 290 sun kamu da korona, jimilla 46,867
Karin 'yan Najeriya 290 sun kamu da korona, jimilla 46,867
Asali: Twitter

Lagos-82

Plateau-82

Oyo-19

FCT-18

Edo-16

Kaduna-15

Enugu-9

Ogun-9

Kano-8

DUBA WANNAN: Yadda wani masanin magunguna ya mutu yayin gasar lalata da karuwa a otel

Kwara-8

Cross River-5

Ondo-5

Rivers-5

Ekiti-4

Imo-3

Borno-2

Alkalluman da hukumar ta dakile cututtukan ta fitar a ranar Litinin 10 ga watan Agusta shekarar 2020 ya nuna cewa jimillar wadanda suka kamu da cutar ta korona a kasar 46,867.

An sallami mutum 33,346 bayan an tabbatar da sun warke sarai, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 950.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel