Yanzu-yanzu: Cutar Korona ta sake harbin yan Najeriya 591 yau, saura kira a kai 40,000
Hukumar hana yaduwar cututtuka a Najeriya wato NCDC ta bayyana cewa annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 591 a fadin Najeriya.
Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da hukumar NCDC ta fitar da misalin karfe 11:34 na daren ranar Juma'a 24 ga Yulin shekarar 2020.
A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa an samu karin sabbin mutane 591 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka:
Oyo-191
Lagos-168
FCT-61
Ondo-29
Osun-26
Ebonyi-24
Edo-23
Ogun-14
Rivers-13
Akwa Ibom-12
Kaduna-10
Katsina-6
Borno-4
Ekiti-3
Delta-3
Imo-3
Niger-1
Kawo yanzu:
Adadin wadanda suka kamu - 39,539
Adadin wadanda suka warke - 16,559
Adadin wadanda suka mutu - 845
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng