Yanzu-yanzu: Sabbin mutane 627 sun kamu cutar Korona a Najeriya, jimilla 15,000
Hukumar Yaki da Cututtuka a Kasa NCDC ta ce annobar cutar Korona ta sake harbin sabbin mutane 627 a fadin Najeriya.
Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da NCDC ta fitar da misalin karfe 11:44 na daren ranar Juma’a, 12 ga watan Yuni na shekarar 2020.
A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa karin sabbin mutum 627 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka;
Lagos-229
FCT-65
Abia-54
Borno-42
Oyo-35
Rivers-28
Edo-28
Gombe-27
Ogun-21
Plateau-18
Delta-18
Bauchi-10
Kaduna-10
Benue-9
Ondo-8
Kwara-6
Nasarawa-4
Enugu-4
Sokoto-3
Niger-3
Kebbi-3
Yobe-1
Kano-1
Jimilla: 15181
An sallami 4891
399 sun mutu
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng