Karin mutum 553 sun harbu da korona a Najeriya, jimilla 9855

Karin mutum 553 sun harbu da korona a Najeriya, jimilla 9855

Hukumar Yaki da Cututtuka Masu Yaduwa a Kasa (NCDC) ta ce annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 553 a fadin Najeriya.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da NCDC ta fitar da misalin karfe 11.55 na daren ranar Asabar, 30 ga watan Mayun na shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa karin sabbin mutum 553 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka;

Lagos-378

FCT-52

Delta-23

Edo-22

Rivers-14

Ogun-13

Kaduna-12

DUBA WANNAN: Katsina: Mutum 13 sun mutu yayin da mutanen gari suka fafata ta 'yan bindiga

Kano-9

Borno-7

Katsina-6

Jigawa-5

Oyo-5

Yobe-3

Plateau-3

Osun-1

Alkalluman da hukumar ta NCDC ta fitar a ranar Asabar 30 ga watan Mayun 2020 ya nuna cewa jimillar wadanda suka kamu ta cutar ta korona a kasar 9855.

An sallami mutum 2856 bayan an tabbatar da sun warke sarai, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 273.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164