Karin mutum 553 sun harbu da korona a Najeriya, jimilla 9855
Hukumar Yaki da Cututtuka Masu Yaduwa a Kasa (NCDC) ta ce annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 553 a fadin Najeriya.
Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da NCDC ta fitar da misalin karfe 11.55 na daren ranar Asabar, 30 ga watan Mayun na shekarar 2020.
A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa karin sabbin mutum 553 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka;
Lagos-378
FCT-52
Delta-23
Edo-22
Rivers-14
Ogun-13
Kaduna-12
DUBA WANNAN: Katsina: Mutum 13 sun mutu yayin da mutanen gari suka fafata ta 'yan bindiga
Kano-9
Borno-7
Katsina-6
Jigawa-5
Oyo-5
Yobe-3
Plateau-3
Osun-1
Alkalluman da hukumar ta NCDC ta fitar a ranar Asabar 30 ga watan Mayun 2020 ya nuna cewa jimillar wadanda suka kamu ta cutar ta korona a kasar 9855.
An sallami mutum 2856 bayan an tabbatar da sun warke sarai, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 273.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng