Covid-19: Karin mutum 176 sun kamu, jimilla 5,621
Hukumar Yaki da Cututtuka Masu Yaduwa a Kasa (NCDC) ta ce annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 176 a fadin Najeriya.
Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da NCDC ta fitar da misalin karfe 11.56 na daren ranar Asabar, 16 ga watan Mayun na shekarar 2020.
A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa karin sabbin mutum 176 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka;
95-Lagos
31-Oyo
11-FCT
8-Niger
8-Borno
6-Jigawa
DUBA WANNAN: PDP ta dakatar da Hunkuyi, Dogara da wasu 'ya'yanta 5
4-Kaduna
3-Anambra
2-Edo
2-Rivers
2-Nasarawa
2-Bauchi
1-Benue
1-Zamfara
Alkalluman da hukumar ta NCDC ta fitar a ranar 16 ga watan Mayun 2020 ya nuna cewa jimillar wadanda suka kamu ta cutar ta korona a kasar 5,621.
An sallami mutum 1,472 bayan an tabbatar da sun warke sarai, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 176.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng