Covid-19: Karin mutum 176 sun kamu, jimilla 5,621

Covid-19: Karin mutum 176 sun kamu, jimilla 5,621

Hukumar Yaki da Cututtuka Masu Yaduwa a Kasa (NCDC) ta ce annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 176 a fadin Najeriya.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da NCDC ta fitar da misalin karfe 11.56 na daren ranar Asabar, 16 ga watan Mayun na shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa karin sabbin mutum 176 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka;

95-Lagos

31-Oyo

11-FCT

8-Niger

8-Borno

6-Jigawa

DUBA WANNAN: PDP ta dakatar da Hunkuyi, Dogara da wasu 'ya'yanta 5

4-Kaduna

3-Anambra

2-Edo

2-Rivers

2-Nasarawa

2-Bauchi

1-Benue

1-Zamfara

Alkalluman da hukumar ta NCDC ta fitar a ranar 16 ga watan Mayun 2020 ya nuna cewa jimillar wadanda suka kamu ta cutar ta korona a kasar 5,621.

An sallami mutum 1,472 bayan an tabbatar da sun warke sarai, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 176.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel