Yanzu-yanzu: Sabbin Mutane 146 sun kamu da Coronavirus, Legas da Kano a gaba

Yanzu-yanzu: Sabbin Mutane 146 sun kamu da Coronavirus, Legas da Kano a gaba

Hukumar yaki da cututtuka masu yaduwa a kasa (NCDC) ta ce annobar cutar covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 146 a fadin Najeriya.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da NCDC ta fitar da misalin karfe 11:55 na yammacin ranar Talata, 12 ga watan Mayu, 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na tuwita, ta sanar da cewa karin sabbin mutane 146 din sun fito daga jihohin Najeriya kamar haka;

57-Lagos, 27-Kano, 10-Kwara, 9-Edo, 8-Bauchi, 7-Yobe, 4-Kebbi, 4-Oyo, 3-Katsina, 3-Niger, 2-Plateau, 2-Borno, 2-Sokoto, 2-Benue, 1-Gombe, 1-Enugu, 1-Ebonyi, 1-Ogun, 1-FCT, 1-Rivers

A yau, an sallami mutane 57 bayan sun samu waraka kuma an yi rashin mutane 8.

KU KARANTA: Jerin Jihohin da su ka samu fiye da Jakada guda a sababbin nade-naden da aka yi

NCDC ta ce ya zuwa karfe 11:55 na yammacin ranar Talata, 12 ga watan Mayu, akwai jimillar mutane 4787 da aka tabbatar da cewa suna dauke da kwayar cutar covid-19 a fadin Najeriya.

An sallami mutane 959 bayan an tabbatar da sun warke sarai, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 158.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng