Sunayen jakadu 42 da Buhari ya ke neman majalisar dattawar ta amince da su

Sunayen jakadu 42 da Buhari ya ke neman majalisar dattawar ta amince da su

- Shugaba Buhari ya tura sunayen jakadu 42 zuwa majalisar dattawa

- Shugaban kasar ya nemi majalisar ta tabbatar tare da tantance su

- Sanata Ahmed Lawan ne ya karanta wasikar Buhari a zauren majalisar yayin zamanta na ranar Talata

A ranar Talata, 12 ga watan Mayu, shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya tura wa majalisar dattawa ta Najeriya sunayen jakadu 42 da zai nada domin ta tantance su.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari tare da sakataren gwamnatin tarayya; Boss Mustapha
Shugaban kasa Muhammadu Buhari tare da sakataren gwamnatin tarayya; Boss Mustapha
Asali: Facebook

Shugaban majalisar dattawa, Sanata Ahmad Lawan, shi ne ya bayyana hakan yayin zaman majalisar da aka gudanar a yau.

A yayin zaman majalisar, Sanata Lawan ya karanta wasikar da shugaban kasar ya aiko musu mai dauke da kwanan watan ranar 6 ga Mayu, 2020.

KARANTA KUMA: Coronavirus: Sanatocin Najeriya sun saba dokar ba da tazara a zaman majalisa

A cewar Buhari, bukatarsa ta yi daidai da sashe na 171 (1), (2) (c) da sashi na (4) cikin kundin tsarin mulkin kasa da aka yi wa kwaskwarima a shekarar 1999.

Ga jerin sunayen zababbun jakadun 42 da Buhari ya tura wa majalisar dattawa da kuma jihohin da suka fito:

  1. C.O. Nwachukwu (Abia);
  2. A. Kefas (Adamawa);
  3. R.U Brown (Akwa Ibom);
  4. G.A Odudigbo (Anambra);
  5. O.C Onowu (Anambra);
  6. Y.S. Suleiman (Bauchi);
  7. E.S. Agbana (Bayelsa);
  8. B.B.M. Okoyen (Bayelsa);
  9. G.M. Okoko (Benue);
  10. A.M. Garba (Borno);
  11. M.I. Bashir (Borno);
  12. M.O. Abam (Cross River);
  13. A.E. Allotey (Cross River);
  14. G. E. Edokpa (Edo);
  15. A. N. Madubuike (Enugu);
  16. Adamu Lamuwa (Gombe);
  17. Mr. Innocent A. Iwejuo (Imo);
  18. M. S. Abubakar (Jigawa);
  19. Y. A. Ahmed (Jigawa);
  20. S. D. Umar (Kaduna);
  21. A. Sule (Kano);
  22. G. Y. Hamza (Kano).
  23. N. Rimi (Katsina);
  24. L. S. Ahmed-Remawa (Katsina);
  25. M. Manu (Kebbi);
  26. I. R. Ocheni (Kogi);
  27. I. A. Yusuf (Kogi);
  28. M. Abdulraheem (Kwara);
  29. W. A. Adedeji (Lagos);
  30. A. U. Ogah (Nasarawa);
  31. A. A. Musa (Niger);
  32. N. A. Kolo (Niger);
  33. S.O. Olaniyan (Ogun);
  34. A. R. Adejola (Ogun);
  35. O. E. Awe (Ondo);
  36. O. O. Aluko (Osun);
  37. I. A. Alatishe (Osun);
  38. V. A. Adeleke (Oyo);
  39. M. S. Adamu (Plateau);
  40. I. N. Charles (Rivers);
  41. Z. M. lfu (Taraba); da
  42. B. B. Hamman (Yobe).

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel