Saboda azumin Ramadan shi yasa nake rokon Buhari ya sassauta mana dokar ta baci – Ganduje

Saboda azumin Ramadan shi yasa nake rokon Buhari ya sassauta mana dokar ta baci – Ganduje

Gwamnan jahar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana dalilan da suka sa yake rokon gwamnatin shugaba Buhari ta sassauta ma jama’an Kano dokar hana fita da ta kakaba musu.

Daily Nigerian ta ruwaito a ranar Alhamis ne Ganduje ya yi wannan kira yayin da yake rantsar da wani kwamitin kwararru da za su taimaka ma kwamitin yaki da COVID19 na jahar Kano.

KU KARANTA: Yabon gwani ya zama dole: Jahohi guda 3 da suka ciri tuta wajen yaki da COVID19 a Najeriya

A jawabinsa, Ganduje ya roki Buhari ya rage kwanaki 14 da ya sanya ma jahar Kano na ba shiga ba fita, saboda a cewarsa hakan zai rage wahalhalu a jahar, musamman a watan Ramadan.

Saboda azumin Ramadan shi yasa nake rokon Buhari ya sassauta mana dokar ta baci – Ganduje
Ganduje Hoto: Shafin Salihu Tanko Yakasai
Asali: Twitter

“Za mu zauna da kwamitin yaki da COVID19 na shugaban kasa don neman izinin sassauta dokar ta bacin da aka sanya ma Kano, muna wannan kira ne a madadin jama’anmu wanda a yanzu haka abincinsu ya kare.

“Muna kira ga gwamnatin tarayya ta sassauta dokar na dan wani lokaci don jama’a su samu daman sayen abinci, musamman a yanzu da yawancin mu suke azumi, hakan zai rage radadin da ake ciki.” Inji shi.

Sai dai a wannan rana da Ganduje yake wannan roko, sai ga shi an samu karin mutane 80 da suka kamu da cutar Coronavirus a jahar Kano, wanda ya kawo jimillan masu cutar zuwa 219.

A wani labari kuma, Gidauniyar Kwankwasiyya, ta Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ta bayyana damuwarta bisa yadda gwamnan Kano, Ganduje ya yi biris da kyautar da ta baiwa jahar.

Kimanin kwanaki 10 da suka gabata ne Kwankwaso ya sanar da bai wa gwamnatin jahar Kano kyautar wani asibiti da ya gina mai suna Amana domin a dinga killace masu cutar Coronavirus.

Asibitinyana nan ne a kan titin Miller, kuma yana cin gado 30 ne, kamar yadda kaakakin dan takarar gwamnan Kano a PDP, Abba Yusuf, Ibrahim Adam ya sanar a ranar 20 ga watan Afrilu.

Sanawar ta kara da cewa asibitin na cike ne da kayan aiki, wadanda Kwankwaso ya sanya a ciki tun zamanin da yake majalisar dattawa.

Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa

ko a http://twitter.com/legitnghausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.com Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com

Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng