COVID-19: Gwamnatin Kano za ta rufe wasu kasuwannin jihar

COVID-19: Gwamnatin Kano za ta rufe wasu kasuwannin jihar

Gwamnatin jihar Kano, karkashin jagorancin Gwamna Abdullahi Ganduje ta ce za ta rufe wasu daga cikin kasuwannin da ke jihar tare da tsananta dokar hana shiga da fice a kan iyakokinta.

Hakan kuwa ya faru ne sakamakon bullar muguwar cutar coronavirus a jihar a ranar Asabar.

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, ya shaidawa BBC cewa tuni aka killace wanda aka samu da cutar a asibitin Pfizer na kwanar Dawaki.

Dan shekaru 75 din da haihuwa na nan a killace don hana yaduwar cutar a jihar.

Ganduje ya ce, ya zama dole gwamnatin jihar ta dauki matakai masu tsanani don hana cinkoson jama'a duk da hakan zai iya takura al'ummar jahar.

A halin yanzu, jihar Kano ta zama cikin jihohin Arewa da aka samu bullar muguwar cutar tun bayan bullar cutar a jihohin Kaduna da Katsina.

COVID-19: Gwamnatin Kano za ta rufe wasu kasuwannin jihar
COVID-19: Gwamnatin Kano za ta rufe wasu kasuwannin jihar
Asali: UGC

KU KARANTA: Gobara ta lashe gidan man Aliko da ke Kano (Bidiyo)

Wani rahoto da jaridar Daily Trust ta wallafa ya bayyana cewa mutumin da ke dauke da cutar coronavirus a jihar Kano ya je sallar Juma'a a Masallaci.

Wannan lamarin kuwa ya jawo rudani da tsananin tashin hankali ga manyan jami'an gwamnatin jihar.

Idan zamu tuna, jihar Kano din ta samu mutum na farko mai dauke da cutar ne a ranar Asabar, 12 ga watan Afirilu.

An gano cewa an kwantar da mutumin ne a wani asibiti mai zaman kansa da ke GRA Nasarawa a jihar Kano.

Wata majiya daga asibitin ta bayyana cewa an kwashe dukkan ma'aikata da majinyatan asibitin inda aka killacesu.

An gano cewa, an kara da kwashe wasu masu makwabtaka da asibitin don gwaji.

Majinyacin dai yana da shekaru 75 kuma tsohon jakada ne. Ya isa Kano ne daga Legas, inda ake zargin ya debo cutar.

Wani mazaunin yankin ya bayyana cewa, kanwarsa da aka aika an hana ta shiga gidan iyalan mutumin.

Hadiman gidan tare da iyalansa da ke kwatas din Giginyu duk an kwashe su zuwa cibiyar killacewa.

Hankalin jama'a mazauna wurin ya matukar tashi bayan gano cewa mutumin na dauke da cutar.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel