Yanzu-yanzu: An samu karin masu cutar Coronavirus 16, Jimilla 305

Yanzu-yanzu: An samu karin masu cutar Coronavirus 16, Jimilla 305

Cibiyar takaita yaduwar cututtuka a Najeriya NCDC ta sanar da cewa an samu karin mutane goma sha bakwai (17) da suka kamu da cutar Coronavirus (#COVID19) a Najeriya a ranar Jumaa, 10 ga Afrilu, 2020.

Cibiyar ta bayyana hakan a shafin ra'ayinta na Tuwita inda tace: “An tabbatar da mutane goma sha shida(16) sun kamu da #COVID19 a Najerya,

8 a Lagos

3 a Katsina

2 a Abuja

1 a Neja

1 a Kaduna

1 a Anambra

1 a Ondo

“Kawo karfe 9:30 na yammacin 10 ga Afrilu, mutane 305 aka tabbatar sun kamu da COVID-19 a Najeriya, an sallami mutane 58, kuma mutane 7 a rigamu gidan gaskiya.“

Yanzu-yanzu: An samu karin masu cutar Coronavirus 16, Jimilla 305
Yanzu-yanzu: An samu karin masu cutar Coronavirus 16, Jimilla 305
Asali: Facebook

A yau, Juma'a, ne shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya gana da kwamitin 'ko ta kwana' da ya kafa a kan annobar cutar covid-19.

A cikin wata sanarwa da shugaba Buhari da kansa ya wallafa a shafinsa na Tuwita, ya bayyana cewa ya na matukar godiya ga kwamitin bisa jajircewarsa a kan aikin da aka dora masa.

Kazalika, ya nuna karfin gwuiwarsa a kan cewa kokarin da kwamitin ya ke yi, zai bawa Najeriya damar samun nasara a kan wannan annoba.

"A yau ne kwamitin ko ta kwana a kan shawo kan annobar cutar covid-19 ya kawo min ziyara domin yi min bayani a kan aiyukansu da halin da ake ciki.

"Ina mai farin ciki da godiya bisa jajircewarsu wajen sauke nauyin da aka dora musu. Ba ni da kokonto ko kadan a kan cewa kokarinsu zai bawa Najeriya damar samun nasara a kan annobar," a cewar Buhari.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel