COVID-19: Buhari zai fara yi wa fursunoni afuwa na musamman a ranar Alhamis

COVID-19: Buhari zai fara yi wa fursunoni afuwa na musamman a ranar Alhamis

A gobe Alhamis 9 ga watan Maris ne gwamnatin tarayya za ta fara sakin fursunonin da shugaban kasa ya yi wa afuwa ta musamman a yunkurin ta na rage cinkoso a gidajen na gyaran hali.

Leadershi ta gano cewa za a fara sakin fursunonin ne bayan amincewar shugaban kasa Muhammadu Buhari da bukatar da ministan harkokin cikin gida, Ogbeni Rauf Aregbesola ya gabatar masa don rake cinkoso a gidajen yarin.

Gwamnatin tarayyar ta Najeriya ta dauki wannan matakin ne domin rage yaduwar cutar coronavirus a kasar.

Buhari zai fara yi wa fursunoni afuwa na musamman a ranar Alhamis
Buhari zai fara yi wa fursunoni afuwa na musamman a ranar Alhamis
Asali: Depositphotos

DUBA WANNAN: Coronavirus: Dole 'yan Najeriya su yi watsi da addini - Guru Maharaj Ji

Wannan sakon na cikin wata takardar gayyata ta musamman ne da ofishin ministan ya aike wa manema labarai na gayyatarsu taro a hedkwatan hukumar kula da gidajen gyaran hali na kasa (NCoS.

Mai magana da yawun hukumar da NCoS, DCC A.C. Njoku ne ya saka hannu a kan sakon.

Ministan zai jagorancin wata tawaga ta musamman zuwa gida gyaran hali na Kuje da ke Abuja domin kaddamar da shirin.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164