COVID-19: Buhari zai fara yi wa fursunoni afuwa na musamman a ranar Alhamis

COVID-19: Buhari zai fara yi wa fursunoni afuwa na musamman a ranar Alhamis

A gobe Alhamis 9 ga watan Maris ne gwamnatin tarayya za ta fara sakin fursunonin da shugaban kasa ya yi wa afuwa ta musamman a yunkurin ta na rage cinkoso a gidajen na gyaran hali.

Leadershi ta gano cewa za a fara sakin fursunonin ne bayan amincewar shugaban kasa Muhammadu Buhari da bukatar da ministan harkokin cikin gida, Ogbeni Rauf Aregbesola ya gabatar masa don rake cinkoso a gidajen yarin.

Gwamnatin tarayyar ta Najeriya ta dauki wannan matakin ne domin rage yaduwar cutar coronavirus a kasar.

Buhari zai fara yi wa fursunoni afuwa na musamman a ranar Alhamis
Buhari zai fara yi wa fursunoni afuwa na musamman a ranar Alhamis
Asali: Depositphotos

DUBA WANNAN: Coronavirus: Dole 'yan Najeriya su yi watsi da addini - Guru Maharaj Ji

Wannan sakon na cikin wata takardar gayyata ta musamman ne da ofishin ministan ya aike wa manema labarai na gayyatarsu taro a hedkwatan hukumar kula da gidajen gyaran hali na kasa (NCoS.

Mai magana da yawun hukumar da NCoS, DCC A.C. Njoku ne ya saka hannu a kan sakon.

Ministan zai jagorancin wata tawaga ta musamman zuwa gida gyaran hali na Kuje da ke Abuja domin kaddamar da shirin.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel