Yanzu-yanzu: An samu karin masu cutar Coronavirus 16, Jimilla 254

Yanzu-yanzu: An samu karin masu cutar Coronavirus 16, Jimilla 254

Cibiyar takaita yaduwar cututtuka a Najeriya NCDC ta sanar da cewa an samu karin mutane goma sha shida (16) da suka kamu da cutar Coronavirus (#COVID19) a Najeriya a ranar Talata, 7 ga Afrilu, 2020.

Cibiyar ta bayyana hakan a shafin ra'ayinta na Tuwita inda tace: “An tabbatar da mutane goma sha shida(16) sun kamu da #COVID19 a Najerya, 10 a Legas, 2 a Oyo, 2 a Abuja, 1 a Delta, 1 a Katsina.“

“Kawo karfe 9:30 na yammacin 7 ga Afrilu, mutane 254aka tabbatar sun kamu da COVID19 a Najeriya, an sallami mutane 44, kuma mutane 6 a rigamu gidan gaskiya.“

DUBA WANNAN: Tashin hankali: Wani dan Najeriya mai Coronavirus ya gantsarawa ma'aikaciyar jinya cizo a fuska

Ga jerin jiha-jiha:

Lagos- 130

FCT- 50

Osun- 20

Oyo- 11

Edo- 11

Bauchi- 6

Akwa Ibom- 5

Kaduna- 5

Ogun- 4

Enugu- 2

Ekiti- 2

Rivers-2

Benue- 1

Ondo- 1

Kwara- 2

Delta- 1

Katsina-1

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng