Yanzu-yanzu: Mutum daya ya sake warkewa daga Coronavirus, an sallameshi

Yanzu-yanzu: Mutum daya ya sake warkewa daga Coronavirus, an sallameshi

- Tabarkallah! An samu karin Mutum daya da ya samu waraka daga muguwar cutar Coronavirus da ta addabi duniya

- Gwamnan jihar Legas ya bayyana cewa sun sallami marasa lafiyan a ranar Asabar

Wani mai fama da cutar Coronavirus dake killace a asibitin cututtuka dake Yaba, Legas ya samu lafiya kuma tuni an sallamesa.

Gwamnan jihar, Babajide Sanwo-Olu ya bayyana hakan ne a hirar da yayi da manema labarai ranar Asabar.

Gabanin yanzu, an sallami mutane 22 bayan an tabbatar da sun warke daga cutar cikin 109 da suka kamu da cutar a jihar. Mutum daya kadai ya mutu.

A fadin tarayya kuwa, cibiyar takaita yaduwar cututtuka a Najeriya NCDC ta sanar da cewa a yanzu, mutane 209 aka tabbatar sun kamu da COVID19 a Najeriya, an sallami 26 , kuma hudu ya rigamu gidan gaskiya.

KU KARANTA: Mutane 7 kacal suka halarci daurin auren diyar gwamnan Jigawa (Hotuna)

Yanzu-yanzu: Mutum daya ya sake warkewa daga Coronavirus, an sallameshi
Mutum daya ya sake warkewa daga Coronavirus
Asali: UGC

A bangare guda,Mutumi mai shekaru 55 a duniya da ya mutu a asibitin koyarwan jami'ar jihar Legas LUTH, Idi Araba, sakamakon cutar Coronavirus bai fadawa ma'aikatan kiwon lafiya gaskiyar abinda yake fama da shi ba lokacin da aka kai shi asibiti.

Majiya a asibitin ya bayyana cewa sai bayan mutuwarsa aka gudanar da gwaji aka gano cewa yana dauke da cutar Coronavirus a jikinsa.

Hakazalika masu jinyarsa suka ki bayyanawa asibitin ainihin abinda ke damunsa da kuma irin tafiye-tafiyen da yayi zuwa kasar waje a makonni baya-bayan nan.

"Amma bayan mai rijistan asibitin ya bayyana masa abubuwan da suka gano a jikinsa, mutumin ya bayyana gaskiyar cewa lallai da yiwuwan ya kamu da cutar COVID-19 saboda tafiyar da yayi kasar waje."

"Ya bayyana cewa tun lokacin da ya dawo daga kasar Holan makonni biyu da suka shude yake fama da tari." Cewar majiyar

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng