Yanzu-yanzu: An samu karin mutane 6 sun kamu da cutar Coronavirus, jimilla 190

Yanzu-yanzu: An samu karin mutane 6 sun kamu da cutar Coronavirus, jimilla 190

Hukumar takaita yaduwar cututtuka a Najeriya NCDC ta sanar da cewa an samu karin mutane shida da suka kamu da cutar Coronavirus (#COVID19) a Najeriya a yau Juma'a, 3 ga Afrilu, 2020.

Hukumar ta bayyana hakan a shafin raayinta na Tuwita ranar Juma'a inda tace: “An tabbatar da mutane shida sun kamu da #COVID19 a jihar Osun, Najerya.“

“Dai-dai Karfe 11:00 na daren 3 ga Afrilu, mutane 190 aka tabbatar sun kamu da COVID19 a Najeriya, an sallami ashirin, kuma biyu ya rigamu gidan gaskiya.“

Ga jerin jiha-jiha:

Lagos- 98

Abuja - 38

Osun- 20

Oyo- 8

Akwa Ibom- 5

Ogun- 4

Edo- 4

Kaduna- 4

Bauchi- 3

Enugu- 2

Ekiti- 2

Rivers-1

Benue- 1

Yanzu-yanzu: An samu karin mutane 6 sun kamu da cutar Coronavirus, jimilla 190
Jjimilla 190
Asali: Facebook

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng