Yanzu-yanzu: An samu karin masu cutar Coronavirus 2 a Abuja, 2 a Legas, 1 a Edo

Yanzu-yanzu: An samu karin masu cutar Coronavirus 2 a Abuja, 2 a Legas, 1 a Edo

Labarin da duminsa na nuna cewa an smau karin masu cutar Coronavirus biyar a Najeriya da safiyar yau Litinin, 23 ga Maris, 2020. Cibiyar NCDC ta tabbatar.

Cibiyar takaita yaduwar cututtuka a Najeriya NCDC ta bayyana hakan ne a shafinta na Tuwita da safiyar Litinin, 23 ga Mairs misalin karfe 09:45 am.

Jawabin yace “An tabbatar da mutane biyar da suka kamu da COVID19: 2 in Abuja, 2 a Lagos & 1 a Edo. 2 sun dawo daga kasar Ingila.“

A yanzu ga adadin masu cutar a jihohi

Lagos- 24

FCT- 6

Ogun- 2

Ekiti- 1

Oyo- 1

Edo- 1

Jimilla: 35

Yanzu-yanzu: An samu karin masu cutar Coronavirus 2 a Abuja, 2 a Legas, 1 a Edo
Yanzu-yanzu: An samu karin masu cutar Coronavirus 2 a Abuja, 2 a Legas, 1 a Edo
Asali: Twitter

A bangare guda, Dan takarar shugaban kasa a karkashin jam'iyyar People's Democratic Party, PDP, a zaben 2019 Atiku Abubakar ya sanar da cewa ɗan sa ya kamu da ƙwayar cutar Covid-19 da aka fi sani da Coronavirus.

Atiku ya sanar da hakan ne a shafinsa na dandalin sanda zumunta na Twitter a ranar Lahadi 22 ga watan Maris na 2020.

Ya rubuta, "Da na ya kamu da ƙwayar cutar Coronavirus."

A cewar tsohon mataimakin shugaban kasar na Najeriya, an garzaya da dan sa zuwa asibitin koyarwa na kwararru da ke Gwagwalada a birnin tarayya Abuja domin yi masa magani.

Ya kara da cewa, "An sanar da hukumar kula da Cututtuka masu saurin yaduwa ta Najeriya @NCDCGov kuma an kai shi asibitin koyarwa na kwararru da ke Gwagwalada a Abuja domin yi masa magani da kulawa da shi.

Zan yi farin ciki idan za ku iya saka shi a addu'o'in ku. Ku cigaba da kiyaye wa domin Coronavirus gaskiya ne."

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng