Yanzu-yanzu: An samu karin masu cutar Coronavirus 10 a Najeriya, 3 a Abuja

Yanzu-yanzu: An samu karin masu cutar Coronavirus 10 a Najeriya, 3 a Abuja

Ministan lafiya, Dakta Osagie Ehanire, ya bayyana cewa an samu karin mutane 10 da suka kamu da cutar Coronavirus a Najeriya.

Ministan ya bayyana hakan ne a shafinsa na Tuwita ranar Asabar, 21 ga watan Maris, 2020.

Yayinda bakwai aka samu a Legas, sauran ukun na birnin tarayya Abuja.

Yanzu dai akwai jimillar masu cutar 22 a Najeriya kuma an sallami biyu da suka samu sauki.

Yanzu-yanzu: An samu karin masu cutar Coronavirus 10 a Najeriya, 3 a Abuja
Yanzu-yanzu: An samu karin masu cutar Coronavirus 10 a Najeriya, 3 a Abuja
Asali: Facebook

Yace “Najeriya ta samu sabbin mutane 10 da suka kamu da cutar Coronavirus a Legas da Abuja. A yanzu haka akwai jimillar mutane 22 a Najeriya: Lagos 16, FCT 3, Ekiti 1 da Ogun 2.An sallami biyu.“

“Dukkansu yan Najeriya ne, 9 sun dawo daga kasar Faransa, Holan, Kanada, Spain da Ingila, daya ya kwasa ne daga wani daga cikinsu.“

“Wadanda ke Abuja ana jinyarsu a asibitin koyarwan jamiar UNIABUJA.“

“Wadanda ke Legas kuma ana jinyarsy a asibitin cututtuka a Legas.“

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel