Yanzu-yanzu: Sanusi yana da 'yancin zuwa ko wane gari, har da Kano - El-Rufai

Yanzu-yanzu: Sanusi yana da 'yancin zuwa ko wane gari, har da Kano - El-Rufai

Gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasiru El-Rufai ya ce Muhammadu Sanusi II , tuɓaɓɓen Sarkin Kano yana da 'yancin tafiya ko wane gari har da Kano.

Bayan cire shi daga sarauta, akwai rahotanni da ke yaɗuwa na cewa ba shi da izinin shiga Kano na a ƙalla watanni uku.

Amma yayin amsa tambayoyin manema labarai a garin Awe a jihar Nassarawa, gwamnan na ya ce kotun babban birnin tarayya ta yanke hukuncin cewa Sanusi yana da ikon tafiya duk inda ya ke so.

Yanzu-yanzu: Sanusi yana da 'yancin zuwa ko wane gari, har da Kano - El-Rufai
Yanzu-yanzu: Sanusi yana da 'yancin zuwa ko wane gari, har da Kano - El-Rufai
Asali: Twitter

El-Rufai ya ce, "Babban kotun ta yanke hukuncin cewa yana da 'yancin zuwa duk inda ya ke so, har da Kano amma ina tunanin yana son ya tafi Legas domin ya tarar da iyalansa."

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel