Tsohon Sarkin Kano, Sanusi, ya jagoranci Sallar Jumaa a Awe (Hotuna)
Tubabben Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya jagoranci Sallar Jumaa yau a babbar Masallacin Awe, dake karamar hukumar Awe, jihar Nasarawa idan aka kaishi.
A bangare guda, Babban kotun tarayya da ke Abuja a ranar Juma'a ta bayar da umurnin sakin tsohon sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II daga inda aka tsare shi a garin Awe na jihar Nasarawa bayan an cire daga kan mulki a ranar Litinin.
Mai shari'ar Anwuli Chikere ne ta bayar da umurnin sakamakon bukatar da shugaban lauyoyinsa, Latee Fagbemi (SAN) ya shigar a ranar Juma'a.
Kotun ta ce a mika takardan umurnin sakin Sanusi da dukkan hukumomin da suka tsare da shi.
Wadanda Sanusi ya yi karar su a kotun kan batun tsare shi suna hada da Sifeta Janar na 'yan sanda, Muhammad Adamu; Shugaban hukumar DSS, Yusuf Bichi; Attony Janar na jihar Kano, Ibrahim Mukhtar da Ministan Shari'a na Najeriya, Mista Abubakar Malami (SAN).

Asali: Facebook

Asali: Facebook

Asali: Facebook
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng