Majalisar dattawa ta gabatar da kudurin da zai hana amfani da injin janareto a Najeriya

Majalisar dattawa ta gabatar da kudurin da zai hana amfani da injin janareto a Najeriya

- Majalisar dattawa ta gabatar da kudurin da zai hana amfani da injin janareto a Najeriya

- Majalisar dai a yau Larabar nan tayi zama na farko akan wannan kuduri, inda idan har ta aminta dashi hakan zai kawo karshen amfani da injin janaretor a fadin Najeriyan

A yau Laraba ne 11 ga watan Maris, majalisar dattawan Najeriya ta gabatar da kudurin da zai hana amfani da injin janareto a Najeriya baki daya.

Kudurin wanda Sanata Bima Muhammadu Emagi, dan majalisa mai wakiltar jihar Neja ta kudu a karkashin jam'iyyar APC, shine ya gabatar da kudurin wanda aka yi zama a kanshi karo na farko a dakin majalisar.

Majalisar dattawa ta gabatar da kudurin da zai hana amfani da injin janareto a Najeriya
Majalisar dattawa ta gabatar da kudurin da zai hana amfani da injin janareto a Najeriya
Asali: UGC

Idan har aka sanya hannu akan dokar, to hakan shine zai kawo karshen amfani da injin janareto a Najeriya baki daya.

To sai dai kuma har yanzu matsalar wutar lantarkin a Najeriya ta zama gado tun iyaye da kakanni har yanzu babu wani canji.

KU KARANTA: 'Yan bindiga sun sace 'yan bautar kasa guda hudu a jihar Katsina

Rashin wutar lantarki tana daya daga cikin babban kalubalen da 'yan Najeriya suke fuskanta shekaru masu yawan gaske.

Wannan dai na zuwa ne yayin da gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari ta nuna cewa tana yin iya bakin kokarinta wajen ganin ta dai-daita lamarin na wutar lantarki a fadin kasar ta Najeriya.

A wani bangaren kuma ana ta faman tataburza a Najeriyan sanadiyyar sauke Sarkin Kano da gwamnatin jihar Kano ta yi a jiya sanadiyyar yiwa gwamnatin rashin da'a kamar yadda gwamnatin jihar ta bayyana.

Mutane dai kowa na fadin albarkacin bakinsa sanadiyyar wannan lamari na bazata wanda babu wanda ya taba tunanin hakan za ta faru.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel