Yanzu-yanzu: Sarkin Bichi, Aminu Ado Bayero, ya zama sabon sarkin Kano

Yanzu-yanzu: Sarkin Bichi, Aminu Ado Bayero, ya zama sabon sarkin Kano

An nada mai martaba sarkin Bichi, Alhaji Aminu Ado Bayero, matsayin sabon sarkin masarautar Kano.

Hakan ya biyo bayan tsige mai martaba sarkin Kano, Muhammadu Sanusi na biyu da gwamnatin jihar Kano tayi.

Hadimin gwamnan Kanon kan sabbin kafafen yada labarai, Salihu Tanko Yakassai, ya bayyana hakan ne ranar Litinin, 9 ga watan Maris, 2020.

Yace: "Majalisar zartarwar jihar Kano ta amince da tsige sarkin Kano, Malam Muhammadu Sanusi II."

Hakazalika, sakataren gwamnatin jihar, Usman Alhaji, ya saki jawabi kan dalilin da yasa gwamnatin jihar ta tunbuke sarkin Kano daga kujerarsa.

Ya ce an kwancewa Sanusi Lamido Sanusi rawani ne saboda yan zubar da mutunci da kuma ko oho da dokokin masarautar.

Baya ga haka, Usman Alhaji ya ce Sarkin ya daina halartan dukkan ganawa da gwamnatin jihar ta shirya ba tare da wani uzuri kwakkwara ba kuma hakan rashin biyayya ne ga gwamnati.

Yace: "Ya kamata a sani cewa a lokuta da dama, Malam Muhammadu Sanusi II ya kasance mai karya sashe na 3 na dokar masarautar kuma idan aka cigaba da zuba masa ido, zai lalata mutuncin masarautar."

"An tunbukeshi ne bayan ganawa da masu ruwa da tsaki a jihar"

Sarkin Kano mai murabus, Malam Muhammadu Sunusi II zai koma jahar Nassarawa domin cigaba da rayuwarsa bayan tsige shi daga kujerar sarautar Kano da gwamnan Kano, Abdullahi Ganduje ya yi.

Jaridar Daily Sun ta ruwaito wata majiya ta karkashin kasa daga fadar Sarkin Kano ta tabbatar mata da cewa zuwa lokacin tattara rahoton nan Sarkin tare da iyalansa sun fara tattara komatsansu da nufin ficewa daga fadar tare da sa idon jami’an tsaro.

Jami’an tsaro da suka hada da Yansanda da na hukumar DSS sun yi masa rakiya har zuwa filin sauka da tashin jirage na jahar Kano, daga nan kuma zasu raka shi zuwa wani gari da ba’a bayyana sunansa ba a jahar Nassarawa don cigaba da rayuwarsa.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng