Yanzun-nan: Gwamnonin PDP sun shiga labule a Abuja

Yanzun-nan: Gwamnonin PDP sun shiga labule a Abuja

- Gwamnonin da aka zaba a karkashin jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) na cikin wata ganawa mai muhimmanci a Abuja

- Suna ganawar ne a masaukin gwamnan jahar Sokoto da ke yankin Asokoro, karkashin jagorancin Shugaban kungiyar gwamnonin PDP, Hon. Aminu Waziri Tambuwal

- An gano wasu daga cikin mambobin kwamitin masu ruwa da tsaki na jam’iyyar ma a wajen taron

Rahotanni sun kawo cewa gwamnonin da aka zaba a karkashin jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) na cikin wata ganawa mai muhimmanci a Abuja.

Ganawar wanda ya fara yan mintuna kadan da suka gabata na wakana ne a masaukin gwamnan jahar Sokoto da ke yankin Asokoro, karkashin jagorancin Shugaban kungiyar gwamnonin PDP, Hon. Aminu Waziri Tambuwal.

Yanzun-nan: Gwamnonin PDP sun shiga labule a Abuja
Yanzun-nan: Gwamnonin PDP sun shiga labule a Abuja
Asali: UGC

Wani hadimin daya daga cikin gwamnonin ya bayyana cewa an kira ganawar ne domin tsayar da magan daya gabannin taron kungiyar gwamnonin Najeriya da za a gudanar a yau Laraba, 26 ga watan Fabrairu, jaridar Tribune ta ruwaito.

A daidai lokacin kawo wannan rahoton an gano wasu daga cikin mambobin kwamitin masu ruwa da tsaki na jam’iyyar a wajen taron.

KU KARANTA KUMA: Yanzu-yanzu: An kai wa shugaban APC na jihar Kwara hari

A wani labari na daban, mun ji cewa Gwamnan Jihar Zamfara, Bello Matawalle ya tarbi kimanin mutane 100,000 da suka sauya sheka daga jam’iyyar APC zuwa jam’iyyarsa a karamar hukumar Zurmi da Shinkafi na Jihar.

A wani jawabi da mai magana da yawun gwamnan, Zailani Bappa, ya rattafa hannu, yace wadanda suka sauya sheka sun koma jam’iyyar PDP ne domin marawa Matawalle baya domin cigaban gwamnatisa.

Wadanda suka sauya shekar sun bayyana cewa sun yanke shawarar komawa PDP ne domin su tabbatar da nasarar da gwamna0n ke samu wajen tabbatar da zaman lafiya da cigaban Jihar.

A jawabansu, shugaban karamar hukumar Zurmi, Auwalu Bawa da tsohon ciyaman din karamar hukumar Shinkafi, Usman Ajiya sun bayyana biyayyar mutane ga gwamnatin Matawalle.

Gwamna Matawalle, a yayin da yake bayyana farin cikinsa kan suaya shekarsu zuwa jami’yyarsa, ya dau alkawarin farantawa kowa rai a Jihar.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng