Tsohon Najadu: Uba ya dirkawa 'yarshi cikin shege har sau biyu ya tsere ya barta da wahala

Tsohon Najadu: Uba ya dirkawa 'yarshi cikin shege har sau biyu ya tsere ya barta da wahala

- Mazaunan garin Okofia, a Otolo Nnewi da ke jihar Anambra sun kori wani mutum mai shekaru 60 daga garin

- An zargi dattijon da dirkawa 'yar cikinshi cikin shege har sau biyu

- Mutanen garin sun yanke hukuncin korar mutumin da 'yar shi din daga garin kwata-kwata

Mazaunan Okofia, a Otolo Nnewi da ke jihar Anambra sun kori wani mutum mai shekaru 60 daga garin. Sun yi hakan ne bayan da aka kama shi da laifin dirkawa 'yarshi ciki har sau biyu.

Daga hotunan da aka wallafa a kafar sada zumunta ta Facebook, an ga hoton dattijon da ake zargi a Okija, karamar hukumar Ihiala, da igiya daddaure da wuyanshi.

Tsohon Najadu: Uba ya dirkawa 'yarshi cikin shege har sau biyu ya tsere ya barta da wahala
Tsohon Najadu: Uba ya dirkawa 'yarshi cikin shege har sau biyu ya tsere ya barta da wahala
Asali: Facebook

'Yar shi tana rike da yarinya mace. Tana daddaure da igiya a kafarta don nuna ta tafka abun kunya.

KU KARANTA: Mune muka tsugunna muka haifi Kannywood, kuma sakacin mu ne yasa ta ruguje - Kamaye na Dadin Kowa

Tsohon Najadu: Uba ya dirkawa 'yarshi cikin shege har sau biyu ya tsere ya barta da wahala
Tsohon Najadu: Uba ya dirkawa 'yarshi cikin shege har sau biyu ya tsere ya barta da wahala
Asali: Facebook

Mahaifin da 'yar sun samu rakiya har wajen motar da ke jiransu kuma tana cike da kayayyakinsu wadanda 'yan garin suka tattara musu.

"Yanzu haka a Okofia Otolo Nnewi, a wajen kwalejin kiwon lafiya ta Unizik. Wannan mutumin da kuke gani ya dirkawa 'yar shi ciki a kashi na biyu. An bukaci da su bar garin Nnewi."

Tsohon Najadu: Uba ya dirkawa 'yarshi cikin shege har sau biyu ya tsere ya barta da wahala
Tsohon Najadu: Uba ya dirkawa 'yarshi cikin shege har sau biyu ya tsere ya barta da wahala
Asali: Facebook

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng