'Yan sanda a Dubai za su yiwa karuwan Najeriya kwasar kaji bayan sun samu gawar wani Balarabe da ya mutu a yayin da yake lalata da wata karuwa

'Yan sanda a Dubai za su yiwa karuwan Najeriya kwasar kaji bayan sun samu gawar wani Balarabe da ya mutu a yayin da yake lalata da wata karuwa

- Bayan mutuwar wani Balarabe da ya kwanta da wata karuwa a kasar Dubai

- Yanzu gwamnatin kasar ta yanke shawarar kama duk wata mace mai zaman kanta da aka gani a kasar

- Bayan an kama su za a mayar da su kasashen su, dalilin wannan lamari da ya faru

Hukumar 'yan sanda ta Hadaddiyar Daular Larabawa sun gama shiri tsaf domin tarkato kan karuwai masu zaman kansu a kasar, bayan sun samu gawar wani Balarabe da ya mutu a lokacin da yake zina da wata karuwa a Otel.

Wannan lamari dai ya faru a yankin Hilly Tower Sharjah, hakan ya sanya aka sanar da 'yan sanda su kama wasu mata dake yankin da ake tunanin karuwai ne.

A wani bidiyo da aka sanya a shafukan sadarwa, jaridar Information Nigeria ta gano cewa an umarci 'yan sandan kasar da su tattaro duka mata 'yan Afirka da suke zaman kasu a kasar, bayan mutuwar wannan Balarabe.

KU KARANTA: Hotuna: Matashin saurayi mai basira ya kera sabuwar mota a Najeriya

Ga dai abinda mutumin da ya wallafa bidiyon yake cewa:

"Karuwa 'yar Najeriya ta kwanta da Balarabe ya mutu a lokacin da yake lalata da ita. Yanzu gwamnatin Dubai za su dawo da duk wata bakar mace da suka gani tana yawo akan titi.

"Lamarin ya faru jiya a yankin Hilly Tower Sharjah, abin babu dadin ji, yanzu haka an kama kusan mata 18."

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng