Masu shara sun tsinci jariri sabon haihuwa a wajen zubar da shara

Masu shara sun tsinci jariri sabon haihuwa a wajen zubar da shara

Rahotanni sun kawo cewa wani jinjiri da aka jefar a wajen zubar da shara a Owerri, babban birnin jihar Imo ya mutu.

Jinjirin ya mutu ne a safiyar ranar Juma’a, 20 ga watan Satumba, a wajen zub da shara dake yankin Hardel Junction, wajen da aka yasar da shi.

An sami jini a jikin jinjirin wanda hakan ya nuna cewa a lokacin ne aka haife shi. An tsince jinjirin ne a cikin kwali ba tare da tufafi ba a jikinsa.

Majiya sun fada ma manema labarai cewa masu sharan titi ne suka tsince shi a mace.

Lamarin ya janyo cunkoso a mahadin hanyan yayinda masu moci da matafiya ke yunkurin kallon mataccen jinjirin.

KU KARANTA KUMA: Yanzu Yanzu: Atiku ya rubuta budaddiyar wasika zuwa ga yan Najeriya, ya sha alwashin samun nasara a kotun koli

Jaridar Punch ta ruwaito cewa an gano yan sanda a wajen da lamarin ya afku.

Ba a sami kakakin rundunar yan sandan jihar, Orlando Ikeokwu ba a waya domin jin karin bayani, amman wani babban jami’in dan sanda ya fada ma manema labara cewa yan sanda na kan gudanar da bincike kan lamarin.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng