Hukumar yan sanda ta damke yan daba 100 a jihar Kano (Hotuna)
Hukumar yan sandan jihar Kano ta bayyana yan daba 100 da aka damke kan laifuka daban-daban da suka aikata, Kwamishanan yan sandan jihar, Ahmed Iliyasu, ya laburta.
Jami'an atisayen Puff Adder na hukumar sun fita sintiri kwanaki 20 bayan bikin babbar Sallah.
Kwamishana yan sandan, Iliyasu, ya ce an damkesu kan kan laifukan garkuwa da mutane, fashi da makami, damfarar yanar gizo.
Yace: "Dukkan yan barandan da suka ki tuba ba zamu samu wajen buya a jihar Kano ba kuma muna basu shawaran cewa su fita daga jihar idan ba haka ba, za'a kamasu kuma zasu fuskanci fushin hukuma."
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng