Da dumi dumi: El-Rufai ya sanar da sunayen sabbin kwamishinoni guda 11
Gwamnan jahar Kaduna, Malam Nasir Ahmad El-Rufai ya mika ma majalisar dokokin jahar sunayen mutane goma sha daya da yake muradin nadasu kwamishinoni, domin majalisa ta tantancesu.
Legit.ng ta ruwaito kaakakin majalisar dokokin jahar, Aminu Shagali ne ya bayyana haka yayin da ya bayyana ma takwarorinsa takardar da gwamnan ya aiko masa dake kunshe da sunayen kwamishinonin a ranar Laraba, 3 ga watan Yuli.
KU KARANTA: Gungun yan bindiga sun yi garkuwa da shugaban kwalejin kimiyyar lafiya
Ga jerin sunayen kwamishinonin kamar haka:
Ja’afaru Sani – Ma’aikatan kananan hukumomi
Idris Nyam – Ma’aikatan kasuwanci, kirkire kirkire da kimiyya
Shehu Muhammad – Ma’aikatan ilimi
Husaini Garba – Ma’aikatan muhalli da ma’adanan kasa
Kabiru Mato – Ma’aikatan wasanni
Balaraba Aliyu-Inuwa – Ma’aikatan ayyuka
Samuel Aruwan – Ma’iakatan tsaron cikin gida da al’amuran cikin gida
Fausat Ibikunle – Ma’aikatan gidaje da cigaban birane
Muhammad Saidu – Ma’aikatan kudi
Hafsat Bello – Ma’ikatan walwalar jama’a da cigaban al’umma
Aisha Dikko – Ma’aikatan shari’a.
Kammala karanto sunayen keda wuya, said an majalisa Samuel Ubankato ya nemi majalisar ta gayyaci mutanen da El-Rufai ya aiko sunayensu dasu bayyana gaban majalisar a ranar Alhamis, 4 ga watan Yuli domin su fara tantancesu, na da nan dan majalisa Mohammed Ahmed ya goyi bayan hakan.
Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa
ko a http://twitter.com/legitcomhausa
KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.com Hausa cikin sauki
Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com
Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa
Asali: Legit.ng