Ku karbe ragamar shugabanci a kasar – Obasanjo ga matasa
- Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo, ya bukaci matasa da su nemi takarar mukaman shugabanci a kasar
- Obasanjo ya bukaci matasan da kada su bari kowa ya yaudare su da cewar sun yi kankanta wajen neman shugabanci
- Jigon kasar ya nuna damuwa kan yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a Najeriya
Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo jiya Alhamis, 27 ga watan Yuni, ya bukaci matasa da su nemi takarar mukaman shugabanci a kasar.
Yayin da ya karbi bakuncin mambobin kungiyar matasan Najeriya a gidansa da ke harabar dakin karatunsa a Abeokuta, Obasanjo ya ce: “kada ku bari kowa ya fada muku cewa kun yi kankanta da neman shugabanci, na soma bada gudumuwana a duniya a lokacin da nake aiki a kasar Congo a shekarar 1960, a lokacin ina dan shekaru 24.
"A lokacin da na tafi filin daga na kasance dan kasa da shekara 35, a lokacin ne na zama shugaban kasa a mulkin soja, ban kai shekaru 40 ba a lokacin."
KU KARANTA KUMA: Majalisar Buhari: Za a bayyana sunayen ministoci a watan Yuli – Sakataren tarayya
Obasanjo ya nuna damuwa cewa sama da yara miliyan 13 ne basa zuwa makaranta a Najeriya.
Yace: “duk abin da nayi, nayi ne saboda na kasance mai ilimi kuma mai kishin kasar Najeriya.
“Da banyi karatu ba da ban kai matsayin yin abubuwan da nayi ba, a yau ina matukar bakin cikin cewa fiye da yaran Najeriya miliyan 13 wadanda ya kamata suna a makaranta sun bar makaranta.”
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.
Asali: Legit.ng