Sojoji sun hallaka yan bindiga 24 a Kaduna, Kano da Neja

Sojoji sun hallaka yan bindiga 24 a Kaduna, Kano da Neja

Rundunar sojin atisayen Operation Harbin Kunama na jihar Kaduna sun hallaka akalla yan bindiga 24 a jihohin Kaduna, Kano da Neja kuma sun damke 61.

Kwamandan Janar na yankin Division 1, Manjo Janar Faruk Yahya ya bayyana hakan ne a wani hira da manema labarai da ya gudana ranar Laraba, 26 ga Yuni 2019 a hedkwatan hukumar dake jihar Kaduna.

Game da cewarsa, an ceto mutanen da aka sace 20 daga sassan masu garkuwa da mutane kuma sun mayar da su wajen iyalansu.

A jawabinsa, ya yi bayanin cewa yawan sace-sacen mutane, barandaci, dabanci, da ya addabi arewacin Najeriya musamman arewa maso yammaci ya sabbaba kafa atisayen Operation Harbin Kunama da babban hafsan soji, Laftanan Janar Tukur Buratai yayi ranar 1 ga Afrilu, 2019.

Amma ya bukaci al'ummar gari su taimakawa jami'an tsaro da bayanai a kan lokaci ba sai an gama kai hari ba.

KU KARANTA: Hukumar yan sanda ta ceto yan kasar Lebanon uku da aka sace a jihar Rivers

A bangare guda, Dakarun Soji na 120 Task Force Battalion da ke Goniri a jihar Yobe sunyi nasara kashe 'yan ta'adda masu yawa a wani harin kwanton bauna da suka kai musu misalin karfe 6:30 na yammacin ranar Laraba.

Sojojin sun kafa tarko ne inda suka jira 'yan ta'addan suka matso kusa sannan suka yi musu luguden wuta a yayin da suka taho a motoccinsu masu dauke da bindigu guda bakwai.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel