Wajibi ne muyi bincike kan mutuwar Mohammad Mursi - Majalisar dinkin duniya

Wajibi ne muyi bincike kan mutuwar Mohammad Mursi - Majalisar dinkin duniya

Shugaban majalisar dinkin duniya, Antonio Guterres ya bada kariya ga kiran da majalisar tayi na gudanar da bincike mai zaman kanta kan mutuwar tsohon shugaban kasar Misra, Mohammed Mursi.

Mataimakin mai magana da yawun shugaban MDD, Haq Farhan, ya bayyanawa kamfanin dillancin Najeriya NAN a birnin New York cewa Antonio Guterres na tare da duk abinda majalisar dinkin dunya ta fadi.

Farhan wanda ya bada amsa kan tambayar cewa shin me majalisar dinkin duniya za ta ce game da martanin kasar Misra cewa ana kokarin siyasantar da mutuwar Mursi.

Muhammad Mursi, shine zababben shugaban kasar Misra na farko a tarihin kasar, ya rasu ranar Litinin a kotu bayan shekara 6 da yi masa juyin mulki da jefashi gidan yari.

A ranar Talata, kwamishanan majalisar dinkin duniya kan kare hakkin dan Adam, ya yi kira ga bincike mai zurfi kan mutuwar Mursi.

A jawabinsa, mai magan da yawunsa, Rupert Colville, ya ce binciken ya game dukkan abubuwan da suka faru da Mursi cikin shekaru shida da aka tsareshi.

Yace: "Ya kamata a gudanar da bincike mai zaman kanta kuma wacce ba tada alaka da kasar da ta tsareshi. Wajibi ne a gudanar da bincike kan abubuwan da suka faru da suka sabbaba mutuwarsa."

Ma'aikatar harkokin wajen Misra ta mayar da martani kan wannan jawabin cewa majalisar dinkin duniya na kokarin sanya baki cikin harkokin kasar da kuma batwa bangaren shari'arta suna.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng