Allah ya haskaka makwanci: An yi jana'izar Muhammad Mursi da safen nan
An gudanar da jana'izar zababben shugaban kasar Misra na farko, Mohammad Mursi, da safiyar Talata, 18 ga watan Yuni a Kahira, babbar birnin kasar bayan rasuwarsa yayinda yake gurfana a kotu ranar Litinin.
Kungiyoyin kare hakkin bil adama sun yi kira ga bincike mai zaman kanta kan abinda ya kai ga rasuwar tsohon shugaban kasan da akayiwa juyin mulki a shekarar 2013.
Daya daga cikin lauyoyinsa, Abdel Moneim Abdel Maksoud yace: "an birneshi a Medinat Nasr, kudancin Kahira, kuma iyalansa sun hallarar."
An gurfanar da shi a kotu ne bisa ga zargin hada baki da wasu kasashen waje da yan bindiga.
KU KARANTA: Yanayin kasa: Ka saurari shawarar Obasanjo, kungiyar Fulani ta fada wa Buhari
Majiya tyace: "Kotu ta bashi daman yin magana na tsawon mintuna biyar... sai ya fadi kasa cikin keji kuma aka kaishi asibiti a lokacin."
"Ya isa asibiti misalin karfe 4:50 na yamma kuma babu wani alamun rauni a jikinsa."
Daya daga cikin lauyoyin Mursi, Osama El Helw, ya bayyana abinda ya faru a lokacin da ya samu labarin mutuwarsa.
"Mun ji sauran firsunoni na ta bugun keji sun iwun cewa Mursi ya mutu."
Tun lokacin da aka yiwa Mursi juyin mulki a ransr 3 ga Yuli, 2013, shugaban kasar Misra, Abdel Fatah Al Sisi ya fara fito na fito yan kungiyar Ikwan inda aka jefa dubunnai cikin kurkuku.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng