Yanzu-yanzu: Yan Boko Haram sun kan kai hari Borno yanzunnan
Wasu gungun yan kungiyar tada kayar bayan Boko Haram suna kan kai hari barikin soji Gajiram, hedkwatan karamar hukumar Nganzai da ke jihar Borno a daren Litinin domin satar makamai.
Mazauna garin sun bayyana cewa yan ta'addan sun shigo garin cikin motoci tara.
Kakakin rundunar Operation lafiya dole, Kanal Ado Isa, ya tabbatar da wannan rahoto inda yace dakarun sojin sun yi arangama da yan ta'addan.
Majiyoyi sun bayyana cewa yan ta'addan sun kai farmaki barikin sojin inda suka sace manyan makamai kuma suka bankawa wasu sassan barikin wuta.
Wasu rahotannin sun bayyana cewa yan Boko Haramin sun sace magunguna, kayayyakin masarufi kafin wucewa.
Har yanzu ba'a san iyakan wadanda suka rasa rayukansu ba amma an samu labarin mutum daya da ya jikkata sakamakon harbin bindiga.
Wannan harin ya faru ne kimanin sa'o'i 24 bayan harin kunar bakin wake ya hallaka akalla yan kallon kwallo 30 a garin Kanduga.
Gajiram ce hedkwatan karamar hukumar Nganzai, inda mutane daga sassan karamar hukumar ke zaman gudun hijra.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng