Buhari yayi sallar idi a masallacin sansanin Mabilla da ke Abuja (hotuna)

Buhari yayi sallar idi a masallacin sansanin Mabilla da ke Abuja (hotuna)

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya halarci sallar Eid El Filtri a masallacin idi na sansanin Mabilla da ke Abuja a ranar Talata, 4 ga watan Yuni.

Daga cikin wadanda suka halarci masallacin tare da Shugaban kasar sun hada da Shugaban hafsan sojoji Tukur Yusuf Buratai, Shugaban masu rinjaye a majalisar wakilai Frmi Gbajabiamilla, Sanata Kabiru Gaya da kuma Shugaban rundunar yan sandan Najeriya Adamu Mohammed.

Babban limamin sojoji, Kyaftin Yusuf ne ya jagoranci sallar idi a masallacin.

Buhari yayi sallar idi a masallacin sansanin Mabilla da ke Abuja (hotuna)
Buhari yayi sallar idi a masallacin sansanin Mabilla da ke Abuja
Asali: Twitter

A ranar yau Talata ne dai daukacin al'umman Musulmi ke bikin karamar Sallah bayan kammala azumin watan Ramadana na tsawon kwanaki 29.

A baya Legit.ng ta rahoto cewa Shugaba Muhammadu Buhari a jiya Litinin yayi kira ga ‘yan Najeriya da su cigaba da halayyar da suka kasance akai cikin watan Ramadana.

Ya kuma nuna farin cikinsa bisa gudanar da zabe da akayi a kasar cikin kwanciyar hankali da lumuna, duk da cewa anyita hasashen za’a samu tashin hankali lokacin zaben.

KU KARANTA KUMA: Bikin karamar sallah: Hukumar yan sanda ta sanar da hana zirga-zirga a Borno

A sakonsa na goron sallah shugaba Buhari ya yabawa hukumar zabe bisa kokarinta na shirya zabe mai inganci a kasar nan. Kana kuma ya jinjinama ‘yan Najeriya a kan juriya da kuma nuna amincewarsu ga da abinda ake kira dimokuradiyya.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ga masu bukatar manhajar mu na Azumi a wannan wata mai albarka sai a bibiyi wannan shafi https://fb.gg/play/ramadan_ramadan

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng